A gaban mijina Akpabio ya fara neman kwanciya da ni —Sanata Natasha
Published: 28th, February 2025 GMT
Sanata Natasha Akpoti ta zargi Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswil Akpabio da neman yin lalata da ita.
’Yar Majalisar Dattawa daga Jihar Kogi ta bayyana cewa mijinta ma shaida ne a kan yunkurin Akpabio ne yin lalata da ita.
A wata hira da aka yi da ita a tashar talabijin ta Arise a safiyar Juma’a, Sanata Natasha ta ce tun da ta ki amincewa da buƙatar Shugaban Majalisar ya kafa mata ƙahon zuƙa.
A makon da ya gabata ne Natasha ta yinwa Akpabio wankin babban bargo a zauren Majalisar bayan ya sauya mata kujera ba tare da tuntubar ta ba.
Shin Kwankwasiyya ta kama hanyar wargajewa ne? NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar JikiYa ba da umarnin ne bayan da ’yan majalisar suka kada ƙuri’ar amincewa da hakan, domin tabbatar da dokokin zauren Majalisar.
Daga bisani ya tura lamarin ga kwamitin ladabtarwar majalisar ta gudanar da bincike tare da gabatar da rahoto cikin makonni biyu.
Ana cikin haka ne ’yar majalisar ta maka shi a kotu tana neman diyyar Naira biliyan 100.03.
A wata hira da aka yi da ita a tashar talabijin ta Arise a safiyar Juma’a, Sanata ta ce, tana da hujjoji da hotunan saƙonnin da ya aika mata.
’Yar Majalisar ta ce Akpabio ya sha kiran ta ta manhajar WhatsApp, sa’annan ta buƙaci Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta bibiyi wayar da suka yi domin gano gaskiya.
Ta bayyana cewa ta sha neman gabatar da kudiri kan Masana’antar Mulmula Karfe na Ajaokuta a zauren Majalisar amma Akpabio yana kin sanya batun a jerin abubuwan da za a tattauna a majalisar.
Ta ce daga bisani bayan ta nuna damuwarta wasu sanatoci suka bukaci ta je ta yi masa magana saboda muhimmancin masana’antar.
Ta ce, da ta yi masa magana sai ya ce, “Sanata Natsaha, a matsayina ba shugaban majalisar nan, Ni ke da wuƙa da nama. Ya kamata ki ba ni kulawa, domin idan kika kuka da ni za ki samu alherai masu yawa.”
Ta ce, ko da ta bayyana masa cewa ba ta fahimta ba sai ya ce, “ya rage naki.”
Ta ce, “wannan abun da ke faruwa da ni daidai yake da na malamin da ke wahalar da ɗalibarsa saboda ta ƙi kwanciya da shi.”
Ta bayyana cewa tun a shekarar 2023 Akpabio ya fara yi mata wannan mummunan tayi a lokacin da ita da mijinta suka ziyarce shi domin taya shi murnar zagayowar ranar haihuwarsa.
Ta ce “yana rike da hannuna muna zagayawa yana nuna mana cikin gidansa, mijina na biye da mu, sai ce zai soma ce na zo gidansa mu huta.
“Mijina da ke biye da mu ya ji maganar, saboda haka ya hana mu tafiya ƙasar waje ni kadai ko in yi tafiya da Akpabio shi kadai.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: kwanciya da ita Majalisar Dattawa
এছাড়াও পড়ুন:
Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne
Shugaban kasar Venezuela Nicolas Maduro ya bayyana sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio da yake ziyarar aiki a kasar Guyana da cewa, sakarai ne.
A yayin ziyarar da sakataren na harkokin wajen Amurka ya kai zuwa kasar Guyana mai makwabtaka da Venezuela, ya ce, Amurka za ta mayar da martani mai karfi akan Venezuela idan har ta kai wa Guyanan hari.
Rubio ya kara da cewa; Idan haka ta faru, to kuwa Venezuela za ta gwammace kida da karatu a wannan rana.
Amurkan dai ta kulla yarjejeniyar tsaro da kasar ta Guyana a yayin ziyarar da Rubio ya kai.
Shi kuwa shugaban kasar ta Venezuela da yake mayar da martani ya ce; Marco Rubio wawa, ya zo yana yi wa kasar Venezuela barazana daga kasar Guyana, sannan ya kara da cewa; Venezuela ta fi karfin a yi mata barazana, domin ita kasa ce ta ‘yanci.”
Alaka a tsakanin Venezuela ta Amurka ta sake tabarbarewa tun bayan da shugaba Donald Trump ya hau karagar mulki, bayan da ya kara kakaba mata takunkumai, da kuma batun mayar da ‘yan hijirar kasar daga Amurka.