Aminiya:
2025-04-19@21:20:39 GMT

Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano

Published: 28th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da Muƙaddashin Shugaban Ma’aikata kuma Babban Sakataren Tsare-Tsare, Salisu Mustapha, kan badaƙalar zaftare albashin ma’aikata ba bisa ƙa’ida ba.

An umarci Mustapha da ya sauka daga muƙaminsa na Babban Sakataren Tsare-Tsare a Ofishin Shugaban Ma’aikata domin ba da damar gudanar da bincike.

A gaban mijina Akpabio ya nemi kwanciya da ni —Sanata Natasha Buhari ya koma Kaduna da zama bayan shafe shekara 2 a Daura

Gwamna Abba ya amince da naɗa Malam Umar Muhammad Jalo, Muƙaddashin Babban Sakataren REPA, a matsayin Muƙaddashin Shugaban Ma’aikatan jihar har zuwa lokacin da za a kammala binciken lamarin.

Matakin gwamna ya biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da dama da ma’aikatan gwamnati suka yi kan rage albashi ba bisa ƙa’ida da kuma jinkirin biyan albashi a kan lokaci.

A martaninsa, ya jaddada matsayin gwamnatinsa na rashin amincewa da duk wani rashin gaskiya da suka shafi harkokin kuɗi.

Ya kuma yi alƙawarin cewa duk wanda aka samu da hannu a lamarin za a hukunta shi.

“Wannan gwamnati ba za ta lamunci duk wani zalunci a kan ma’aikata ba. Duk wanda aka kama yana wawure albashin ma’aikata za a hukunta shi ba tare da la’akari da muƙaminsa ba,” in ji Gwamna Abba.

Domin shawo kan matsalar, gwamnan ya kafa kwamitin mutum bakwai wanda Kwamishinan Raya Karkara, Abdulkadir Abdussalam, zak jagoranta.

Gwamnan ya bai wa kwamitin umarni da ya duba albashin ma’aikata daga watan Oktoban 2024 zuwa Fabrairun 2025 domin gano waɗanda abin ya shafa, tantance asarar kudade, da bayar da shawarwari kan matakin da ya dace a ɗauka.

An umarci kwamitin da kammala bincikensa cikin kwanaki bakwai tare da gabatar da cikakken rahoto.

An naɗa Salisu Mustapha a matsayin Muƙaddashin Shugaban Ma’aikatan jihar a farkon wannan wata bayan Shugaban Ma’aikata jihar, Abdullahi Musa, ya tafi hutun jinya zuwa ƙasar Indiya domin neman magani.

Gwamna Abba ya tabbatar wa ma’aikatan Jihar Kano cewa gwamnatinsa na da niyyar kasancewa adala, mai gaskiya, da kuma biyan albashi a kan lokaci.

Ya gargaɗi duk wani jami’in gwamnati da ke da hannu a badaƙalar kuɗi cewa zai fuskanci fushin doka.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas, ya fitar da wata sanarwa mai ƙarfi game da yiwuwar dawowar wasu shugabannin siyasa cikin jam’iyyar. A lokacin ganawar da manema labarai a Kano, Abbas ya bayyana cewa APC ba za ta karɓi mutane da hukumomin yaƙi da cin hanci kamar EFCC da ICPC ke bincike ba.

Wannan sanarwa ta zo ne a yayin da jita-jita da ake cewa wasu daga cikin mambobin jam’iyyar NNPP, musamman waɗanda ke cikin rukuni na Kwankwasiyya, suna duba yiwuwar komawa APC.

El-rufa’i Ba Zai Halarci Taron Jam’iyyar APC Na Kasa Ba, Kuma Ganduje Na Nan A Shugabanci  NNPP Ta Mutu, Kwankwaso Zai Sake Dawowa APC – Ganduje

Abbas ya bayyana cewa duk wanda ke son dawo wa jam’iyyar dole ne ya nemi afuwa daga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, bisa maganganun cin mutunci da aka yi a baya akan su da jam’iyyar.

Masu fashin baƙin siyasa na ganin cewa wannan magana ta Abbas tana nufin shugaban Kwankwasiyya, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ake zargin yana cikin tattaunawar yiwuwar sauya sheƙa. Wannan furucin na shugaban APC na Kano ya janyo muhawara game da yadda siyasa da daidaiton ra’ayi za su iya faruwa a cikin tsarin siyasar Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — Shettima
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Rahoton Hana Shettima Shiga Villa
  • Babu wanda ya hana Shettima shiga Aso Rock ba— Fadar Shugaban Ƙasa
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima
  • Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.
  • Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa
  • Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano