Aminiya:
2025-03-30@20:24:33 GMT

Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa

Published: 28th, February 2025 GMT

Cibiyar Bunƙasa Ayyukan Bincike za ta gudanar da gangami domin nazarin dokokin da suka shafi zamantakewar Musulmi a jihohin da ta ke aiki, domin inganta haƙƙoƙin mata da ƙananan yara.

Shugaban tawagar cibiyar, Dokts Taofik Abubakar daga Jami’ar Bayero Kano ne, ya bayyana hakan yayin wata ziyarar girmamawa da suka kai wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, a fadarsa da ke Zariya.

Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki

Dokta Taofik, ya ce sun je fadar ne, domin neman albarka da shawarwari kan hanyoyin magance cin zarafin mata.

Ya kuma bayyana cewa cibiyar ta ɗauki nauyin malamai da limamai zuwa Jami’ar Al-Azhar da ke Masar don ƙaro ilimi kan matsayin Musulunci game da cin zarafin mata.

A cewarsa, cin zarafin mata al’ada ce da aka gada daga tsohuwar ɗabi’a, ba addinin Musulunci ba.

Ya ƙaryata fahimtar da wasu ke da ita cewa Musulunci yana goyon bayan miji ya doki matarsa, inda ya jaddada cewa Annabi Muhammad (SAW), ya haramta hakan.

Cibiyar za ta gudanar da gangamin tattaunawa da shugabannin jihohin Kano da Kaduna domin nazarin dokokin da suka shafi zamantakewar Musulmi, tare da ƙoƙarin tabbatar da su matsayin doka.

A nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya buƙaci a sake nazarin dokar zamantakewar Musulmi da aka yi watsi da ita a Kano, domin inganta haƙƙoƙin mata a Arewacin Najeriya.

Ya bayyana cewa haƙƙoƙin mata ba su da ƙarfi a tsarin dokokin shari’a na yankin, wanda ke haifar da cikas ga rayuwarsu.

Ya ce idan aka tabbatar da dokar, zai taimaka wajen kare haƙƙin mata da yara a Arewa.

Sarkin ya kuma buƙaci da a gaggauta tabbatar da dokar a jihohin da ake gudanar da aikin, domin ta zama doka da za a bi a duk faɗin Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Cibiya Sarkin Zazzau yara Zariya tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya musanta cewa akwai tsamin dangantaka tsakaninsa da Gwamnatin Sakkwato.

Ana iya tuna cewa bayan karɓar akalar jagoranci ne Gwamna Ahmed Aliyu ya yi wa Dokar Masarautar Sakkwato gyaran fuska tare da sauke wasu sarakunan gargajiya, lamarin da aka riƙa raɗe-raɗin wani yunƙuri ne tsige shi kansa Sarkin Musulmin.

Hotunan Sallar Idi daga sassan duniya Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta

Sai dai da yake jawabi a saƙonsa na barka da sallah, Sarkin Musulmi ya ce “ba wata rashin jituwa ko faɗa a tsakaninmu.

“Muna aiki tare a koyaushe. Aikinmu mu taimaka wa gwamnatin [Sakkwato] kan shirye-shiryen da ta ɗauko domin ciyar da jama’a gaba.”

Ya yi kira ga al’ummar musulmi da su ci gaba da yi wa shugabanni addu’a domin samun nasara wajen sauke nauyin jama’a da rataya a wuyansu.

Kazalika, Alhaji Sa’ad ya ce karantarwar addini da aka samu a watan Azumi mai albarka abu ne da ya kamata a riƙe a sanya cikin aiki.

“Mu ƙara ɗaure ɗamara kar mu koma gidan jiya wajen aikata saɓon Allah. Mu dage da yin ibada kar a ja baya. Sannan mu riƙa yi wa shugabanni addu’a.

“Ku kuma shugabanni ku ji tsoron Allah cikin jagoranci. Idan za a yi ayyukan jama’a kar a ji tsoron kowa sai Allah,” in ji Sarkin Musulmi.

Sarkin ya yi kira ga jami’an tsaro da su ktara ƙaimi wajen magance matsalar tsaro domin a cewarsa har yanzu akwai sauran aiki a ba iya Jigar Sakkwato kaɗai ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Talakawa su girmama shugabanni yayin bayyana matsalolinsu — Sarkin Musulmi
  • Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi
  • Dalilin da Aminu Bayero ba zai iya jagorantar hawan Sallah ba — Kurawa
  • Kisan ‘Yan Arewa 16 A Jihar Edo: Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Ta Nemi Adalci
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 
  • Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya
  • Kwankwaso Ya Yi Allah-wadai Da Kisan ‘Yan Arewa A Edo, Ya Buƙaci A Yi Adalci
  • ‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
  • Ɓarayin kekunan ɗinki sun shiga hannu a Borno
  • ECOWAS ta gyara cibiyar magance shan miyagun ƙwayoyi a AKTH