Leadership News Hausa:
2025-03-31@02:14:50 GMT

Majalisa Za Ta Binciki INEC Kan Jinkirin Gudanar Da Zaben Cike Gurbi

Published: 28th, February 2025 GMT

Majalisa Za Ta Binciki INEC Kan Jinkirin Gudanar Da Zaben Cike Gurbi

Ya kara da cewa rashin gudunar da daga wurin INEC abu ne mai hadari, wanda ya saba wa dokokin tsarin mulki da dokoki wadanda suka tilas zaben cike gurbi a duk lokacin da aka samu bukatan hakan.

Rahotanni sun bayyana cewa a halin yanzu akwai kujeru bakwai a majalisar kasar nan da babu kowa, akwar biyar a majalisar wakilai, sannan akwai biyu a majalisar dattawa.

Kujerun da babu kowa a majalisar wakilai akwai a jihohin Edo da Oyo da Kaduna da Ogun da kuma Jigawa, yayin da kujerun majalisar dattawan na jihohin Edo da Anambra.

Biyu daga cikin wadannan kujeru sun zama babu kowa ne bayan zaben gwamnan a Jihar Edo, yayin da sauran biyar suka zama babu kowa saboda mutuwar ‘yan majalisa.

Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebolo da mataimakinsa, Denis Idahosa, sun kasance ‘yan majalisar tarayya da ke wakiltar Edo ta tsakiya a majalisar dattawa da kuma mazabar tarayya ta Obia a majalisar.

Sauran kujerun da ba su da kowa sun hada da na marigayi Sanata Ifeanyi Ubah (Anambra South), Isa Dogonyaro (Jigawa), Ekene Abubakar Adams (Kaduna), Olaide Akinremi (Oyo) da Adewunmi Oriyomi Onanuga (Ogun).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Gudanar Da Faretin Jiragen Ruwa A Tekun Farisa Da Kuma Tekun Caspian Don Raya Ranar Kudud Ta Duniya

Jiragen ruwan yaki na dakarun juyin juya halin musulunci  IRGC a nan Iran, kanana da manya-manya, har’ila yau da na masu sa kai sun gudanar da faretin jiragen ruwan yaki don raya ranar Kudus ta duniya kwana guda kafin ranar.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto dubban  jiragen yaki da na masu sa kai a tekun Farisa da ke kudancin kasar da kuma tekun Caspian da ke arewacin kasar suna jerin gwano a cikin ruwayen yankunansu don raya wannan ranar.

Dakarun IRGC sun gudanar da wannan atisai ne a jiya Alhamis, don nuna goyon bayansu ga Falasdinwa musamman a Gaza, wadanda a halin yanzu, sojojin HKI sun yi masau kawayya, sun hana shigowar abinda da abinsha  cikin yankin sama da wata gusa, sannan suna binsu suna kashewa.

Majiyar dakarun IRGC ta bayyana cewa sama da jiragen ruwa da kwale-kwale kimani 3,000 ne suka fito don tallafawa falasdinawa musamman a Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan, wadanda sojojin yahudawa suka kashewa a ko wace rana.

Labarin ya kara da cewa, a kudancin kasar an baje kolin katafaren jirgin ruwa mai daukar jirage yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa, mai sun a ‘shahida beheshti’, jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa suna sauka su kuma tashi a kan wannan jirgin yakin.

HKI dai wacce take samun tallafin kasashen yamma musamman Amurka suna mamaye da kasar Falasdinu fiye da shekaru 70 a halin yanzu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Fiji: Ya Kamata A Koyi Fasahohin Da Kasar Sin Ta Samu A Fannin Raya Kasa
  • Rikici Ya Turnuke Jam’iyyar SDP A Yayin Da Aka Samu Shugabanni Bangare Biyu A Kogi
  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?
  • Miliyoyin mutane sun gudanar da jerin gwanon ranar Qudus
  • Gwamnatin Edo Za Ta Binciki Kisan Matafiya ‘Yan Arewa A Jihar
  • Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio
  • Ana Gudanar Da Tarukan Ranar Quds Ta Duniya A Wannan Juma’a
  • Iran Ta Gudanar Da Faretin Jiragen Ruwa A Tekun Farisa Da Kuma Tekun Caspian Don Raya Ranar Kudud Ta Duniya