Aminiya:
2025-02-28@20:29:50 GMT

Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara

Published: 28th, February 2025 GMT

Dakarun Sojin ‘Operation FANSAN YANMA’, sun kama Ƙasurgumin Shugaban ’Yan Bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu, wanda ya addabi al’ummar Mada, Tsafe, da wasu yankunan Jihar Zamfara.

Dakarun sun kai farmaki Hegin Mahe, Ruwan Bore, garin Mada, a Ƙaramar Hukumar Gusau a ranar 27 ga watan Fabrairu.

Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano

Bayan musayar wuta, sojoji sun kashe wasu ’yan bindiga, yayin da Nabamamu ya tsere zuwa cikin wani gida, amma daga ƙarshe dakarun suka cafke shi.

Bayan kama shi, ɗaya daga cikin yaransa, Bakin Malam, ya jagoranci kai harin ramuwar gayya wasu ƙauyuka, wanda ya tilasta wa mazauna ƙauyukan tserewa.

Sai dai dakarun sun mayar da martani, inda suka fatattaki ’yan bindigar, tare da ƙara jibge sojoji don tabbatar da tsaro a yankin.

Nabamamu, ya kasance almajiri ne, daga baya ya zama hatsabibin ɗan bindiga wanda ya yi sanadin ajalin mutane masu yawan gaske.

Ya jagoranci sama da mayaƙa 100, inda yake karɓar haraji daga hannun mazauna wasu ƙauyuka, kuma yana da alaƙa da masu yi wa wasu mahara safarar makamai a yankin.

Kama shi na iya rage ƙarfin ’yan bindiga a Zamfara, yayin da sojoji ke ƙara ƙaimi domin kawar da barazanar tsaro da tabbatar da zaman lafiya a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Artabu dakaru Ɗan Bindiga musayar wuta Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Kwankwasiyya ta kama hanyar wargajewa ne?

A ranar Litinin ne Jam’iyyar NNPP ɓangaren Kwankwasiyya a Kano, ta fitar da sanarwar dakatar da jiga-jigan ’yan siyasarta huɗu. 

An dakatar da Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila, da sauran ’yan majalisar wakilai uku, da suka haɗa da Aliyu Sani Madakin Gini da Kabiru Alhassan Rurum da kuma Abdullahi Sani Rogo.

Sai dai ba kowa ne ya san asalin mafarin rigimar ’yan majalisar da madugunnKwankwasiyyam Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ba.

Saɓanin ya faro ne a lokacin da Kwankwaso ya jagoranci fitar da shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli.

 

Yadda kasuwar buƙata ta haɗe su da Kwankwaso a 2023

Dama dai ana ganin Sani Rogo da Kawu Sumaila, asali ba su da gami da tafiyar siyasar Kwankwasiyya, amma saboda kasuwar buƙata ce, suka haɗe daga baya.

Abdullahi Sani Dogo ya koma jikin Kwankwaso ne tun bayan raba gari da tafiyar gidan Malam Ibrahim Shekarau.

Shi kuma Kawu Sumaila, ya koma jikin Kwankwaso ne gab da zaɓen 2023.

Kabiru Alasan Rurum, asali ɗan Kwankwasiyya ne, amma ya bart a a lokacin Gwamnatin Ganduje, har ya zama Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano. Sai dai bayan hana shi takarar gwamna a Jam’iyyar APC, ya koma gidansa na da, wato Kwankwasiyya.

Wanda aka fi yin mamakin saɓaninsa da tsarin Kwankwasiyya shi ne Ali Sani Madakin Gini, ganin yadda a zamanin Ganduje, ya rasa kujerar ɗan Majalisar Tarayya saboda nuna biyayya ga Kwankwaso.

 

Ainihin tushen saɓaninsu da Kwankwaso

Saɓanin ya faro ne a lokacin da Kwankwaso da kansa ya jagoranci fitar da shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli, ba tare da bai wa ɗaya da cikin waɗannan jiga-jigai dama ba.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa, babu wanda aka bai wa dama a cikinsu a fitar da shugabancin ƙananan hukumomin da suka fito, abin da suke ganin tamkar cin fuska ne ga buwayarsu ta siyasa.

Misali da ƙaramar hukumar Sumaila, a yadda aka saba, Kawu Sumaila shi yake kafa shugabanci a matakin ƙaramar hukumar, amma a wannan karon, Kwankwaso ya bai wa Faruk Abdu, ɗan tafiyarsa na asali, wanda kuma bai cika shiri da Kawu Sumaila ba a siyasance.

Tun daga lokacin ake zaman doya da manja, har ake zargin ’yan majalisar da ƙara rura wuta a tafiyar Abba Tsaya da Kafarka da ta kunno kai a kwanakin baya.

 

Makomar siyasar Kwankwasiyya

A yanzu haka, ’yan majalisar da aka dakatar sun barranta kansu da NNPP mai littafi, inda suka bayyana cewa, su ’yan Jam’iyyar NNPP mai kayan marmari ne. Kuma a yanzu haka maganar tana kotu, kan wane ɓangare ne ke da halaccin a matsayin jam’iyya.

’Yan Kwankwasiyya a Kano na kallon ’yan majalisar huɗu a matsayin masu butulci. Misali da Kawu Sumaila da ya daɗe yana neman Sanata bai samu ba, har sai da ya haɗa tafiya tare da Kwankwaso.

Ana ganin Kwankwasiyya ka iya samun rauni, musamman a Kano ta Kudu, idan har aka tafi a haka. Kuma da ma tun a zaɓen 2023, Kwankwasiyya ba ta da ƙarfin a-zo-a-gani a yankin Kano ta Arewa.

Abun jira a gani shi ne ko Kwankwaso zai yafe wa ’yan majalisar, a tunkari zaɓen 2027 tare, tun da dai siyasa kasuwar buƙata ce.

Ko kuma zai zaɓi zama shi ƙadai gayya a zaɓe mai zuwa, kamar yadda ya sha gwadawa a baya tana kai masa.

Idan ko hakan ya zaɓa, tabbas za a doka siyasa, kuma a cikin biyu a yi ɗaya: Walau ya koya musu darasinta, ko kuma su nuna masa ƙarfinsu ya kawo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano
  • Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta ‘Euro-Med Monitor’ Ta Ce Ta Sami Shaidu Wadanda Suka Tabbatar Da Cewa HKI Tana Azabtar Da Fulasdinwa
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara
  • Shugaban kasar Guinea-Bissau a ya yi wata ganawa da shugaban kasar Rasha
  • Shin Kwankwasiyya ta kama hanyar wargajewa ne?
  • NAF Ta Fara Binciken Mutuwar Farar Hula A Yayin Rikici Da Wasu Mutane A Kaduna
  • Mayaƙan Boko Haram sun sace kwale-kwale 8 a Borno
  • DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa