Babu Wani Dan Arewa Mai Hankali Da Zai Yi Wa APC Kamfen A 2027 – PDP
Published: 28th, February 2025 GMT
“PDP jam’iyyar siyasa ce, kuma muddin kuka ci gaba da kai mata hari, ba za ku samu ci gaba ba. Ba za ku iya daukar nauyin ‘yan baranda na siyasa da farfaganda don lalata mana kima ba don kawai burge Shugaba Bola Tinubu saboda ajandar ku ta 2027.
“Ba wani dan Arewa mai hakali da zai yi wa APC yakin neman zabe a Arewa.
“Bai kamata Uba Sani ya bar wasu ‘yan siyasa suna yaudararsa, wadanda ba za su iya amfanar da siyarsa da komai ba.
“Saboda haka, ‘ya’yan jam’iyyarmu da aka zaba a PDP ba su kwanta barci ba. Suna aiki tukuru a mazabarsu fiye da na APC.
“Ba za ku iya yin amfani da nasararmu ta siyasa ta hanyar tallafa wa masu yada farfaganda don bata zababbun ‘yan majalisarmu ko ta hanyar sauya sheka a zai yi tasiri ba,” in ji Dingyadi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Arewa
এছাড়াও পড়ুন:
Babu wanda ya hana Shettima shiga Aso Rock ba— Fadar Shugaban Ƙasa
Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙaryata labarin da karaɗe kafofin sada zumunta cewa sojoji sun hana mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima shiga Fadar Shugaban Ƙasa.
Labarin da ya tayar da ƙura cewa sojojin sun tare ƙofar shiga fadar shugaban ƙasa da cewa umarni ne daga sama ya koma gidansa da ke makwabtaka da fadar shugaban kasa, zuwa lokacin da Shugaba Tinubu ya dawo daga ziyarar aiki da ya kai ƙasar Faransa.
Wata sanarwa da Stanley Nkwocha, hadimin shugaban ƙasa kan yada labarai, ya fitar, ta ce, babu kashin gaskiya a labarin.
Sanarwar ta kara da cewa hasali ma, masu yaɗa labarin karya sun ƙirƙirar shi ne da nufin haddasa saɓani tsakanin shugaban ƙasa Bola Tinubu da mataimakin nasa.