Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna (KSPWA) ta yaba da gudunmuwar da Gwamnatin Jihar Kaduna Malam Uba Sani ya ke badawa wajen samun nasarorin da aka samu kwanan nan.

 

An bayyana hakan ne a yayin wata ziyarar girmamawa da Shugaban Hukumar Jindadi Alhazai na Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar ya jagoranta tare da tawagar Kwamitin Musamman na Hajji da shugabannin ga Sarkin Zazzau, Malam Nuhu Bamalli, a fadarsa da ke Zariya.

 

Babban burin ziyarar shi ne neman ci gaba da samun goyon baya da addu’o’in Sarkin don samun nasarar ayyukan Hajji na shekarar 2025.

 

Malam Salihu ya nuna godiya sosai ga gudunmuwar da Sarkin ya ba da a baya kan shirye-shiryen Hajji, tare da jaddada muhimmancin cigaba da wannan hadin kai.

 

Ya ce, “Goyon bayan Gwamnatin Jihar Kaduna ga jin dadin alhazanmu abin alfahari ne. Tallafi daga dukkan fannoni, ciki har da na kudi ya taimaka mana sosai wajen cimma nasarorinmu. Wannan irin goyon bayan ya bambanta Hukumar ta Kaduna da takwarorinta.”

 

Malam Salihu ya kara da cewa hukumar ta riga ta yi rijistar alhazai 3,480 don lokacin Hajji mai zuwa kuma ta kaddamar da shirin wayar da kan alhazai.

 

Wannan shirin yana da nufin ilmantar da alhazai game da yadda ake gudanar da ibadar Hajji, dokoki, da koyarwar addinin Musulunci.

 

A nasa jawabin, Sarkin Zazzau, Malam Ahmad Nuhu Bamalli, ya yabawa Kwamitin Musamman na Hajji kan gyare-gyaren da suka kawo a hukumar.

 

Ya jaddada cewa wadannan gyare-gyaren suna da matukar muhimmanci wajen tabbatar da cewa alhazan sun amfana da kudaden da suka kashe wajen tafiya Saudiyya.

 

Sarkin ya yi kira da a ilmantar da alhazai kan haramcin daukar kaya haram zuwa Kasar Saudiyya don kauce wa samun matsala da hukumomin Saudiyya.

 

Ya kuma roki Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Saudiyya da su ci gaba da yin aiki tare da Hukumar Hajji ta Kasa domin tabbatar da cewa alhazan Najeriya sun samu kima da mutunci a tsawon zamansu.

 

Rel/Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai Ta Kaduna Ta Nemi Goyon Bayan Sarkin Nasarar

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro

Har ila yau, Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya aike wa hukumomin tsaro wasiƙa yana sanar da shirinsa na gudanar da bikin.

Gwamnatin jihar da masarautar Kano har yanzu ba su ce komai ba kan wannan haramci ba.

Wannan mataki na zuwa ne bayan da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya sanar da soke shirinsa na yin hawan, yana mai cewa sun ɗauki matakin ne bayan shawarar da malamai da dattawa suka ba shi.

“Muna tabbatar muku cewa hawan Sallah ba abu ne na ko a mutu ko a yi rai ba, idan har zai haddasa tashin hankali, wajibi ne a dakatar,” in ji Aminu Ado Bayero.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • Hezbulla: Iran Ce Babbar Mai Goyon Bayan Al-Ummar Falasdinu
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Gobe take Sallah a Nijeriya — Sarkin Musulmi
  • Hamas ta yi Tir da kakkausar murya da harin Isra’ila kan masu aikin ceto a Gaza
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Kisan ‘Yan Arewa 16 A Jihar Edo: Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Ta Nemi Adalci
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • ‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro