An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya
Published: 28th, February 2025 GMT
Hukumomi a Ƙasar Saudiyya, sun tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan da yammacin yau Juma’a.
Hakan na nuni da cewa azumin bana zai fara a ranar Asabar, 1 ga watan Maris, 2025.
Shafin Haramain Sharifain ne, ya tabbatar da wannan sanarwa, yayin da aka ga jinjirin watan a wurare daban-daban na ƙasar.
Wannan na nufin cewa Musulmai a Saudiyya za su fara azumi a ranar Asabar.
Hakazalika, ƙasashen Qatar da Oman sun sanar da cewa za su fara azumin Ramadan a wannan ranar Asabar.
A yayin da ake shirin shiga wannan wata mai alfarma, an yi kira ga Musulmai da su yi amfani da lokacin azumi wajen ƙara yawan ibada, yin kyawawan ayyuka, da taimaka wa marasa galihu, duba da yanayin tattalin arziƙin duniya.
Ana sa ran cewa, Saudiyya da wasu ƙasashe, za a fara azumin Ramadan a sassa daban-daban na duniya a ranar Asabar, 1 ga watan Maris, 2025.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jinjirin Wata Ramadan Saudiyya ranar Asabar
এছাড়াও পড়ুন:
Sarkin Musulmi ya ba da umarnin dubin watan Ramadan
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar ya bayar da umarni ga jama’a da su fara duban jaririn watan Ramadan daga ranar Jumu’a 29 ga watan Sha’aban, 1446 Bayan Hijira, wanda ya yi daidai da 28 ga watan Fabrairu, 2025.
Shugaban Kwamitin Bayar da Shawara kan Harkokin Addini a Fadar Sarkin Musulmi, Wazirin Sakkwato, Farfesa Sambo Wali Junaidu ne ya sanar da hakan a wata takarda da ya raba wa manema labara.
Wazirin Sakkwato ya ce duk wanda ya samu ganin jinjinrin watan Ramadan ya sanar da hakimi ko uban ƙasar da ke kusa da shi.
Daga nan ne za a kai maganar ga Sarkin musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.
Ya roƙi Allah Ya taimake su a cikin wannan aikin da suke yi na addini.
Ramadan shi ne wata na tara a kalandar Musulunci, kuma al’ummar Musulmi na azumtar sa baki ɗaya.
Azumin Ramadan shi ne ka uku a cikin ginshikan addinin Musulunci guda biyar.