Aminiya:
2025-04-21@10:07:14 GMT

An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya 

Published: 28th, February 2025 GMT

Hukumomi a Ƙasar Saudiyya, sun tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan da yammacin yau Juma’a.

Hakan na nuni da cewa azumin bana zai fara a ranar Asabar, 1 ga watan Maris, 2025.

Shafin Haramain Sharifain ne, ya tabbatar da wannan sanarwa, yayin da aka ga jinjirin watan a wurare daban-daban na ƙasar.

Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano

Wannan na nufin cewa Musulmai a Saudiyya za su fara azumi a ranar Asabar.

Hakazalika, ƙasashen Qatar da Oman sun sanar da cewa za su fara azumin Ramadan a wannan ranar Asabar.

A yayin da ake shirin shiga wannan wata mai alfarma, an yi kira ga Musulmai da su yi amfani da lokacin azumi wajen ƙara yawan ibada, yin kyawawan ayyuka, da taimaka wa marasa galihu, duba da yanayin tattalin arziƙin duniya.

Ana sa ran cewa, Saudiyya da wasu ƙasashe, za a fara azumin Ramadan a sassa daban-daban na duniya a ranar Asabar, 1 ga watan Maris, 2025.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jinjirin Wata Ramadan Saudiyya ranar Asabar

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?

Rahotanni na cewa Mataimakin Gwamnan Bauchi, Auwal Mohammed Jatau, ya zabga wa Ministan Harkokin Waje, Yusuf Maitama Tuggar, mari saboda kalaman suka da ya yi kan gwamnatin jihar.

Wasu rahotanni na cewa Ministan ya yi wasu kalamai na caccaka ga Gwamna Bala Mohammed, lamarin da ya fusata mataimakinsa ya ɗauke Ministan da mari.

An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi JAMB ta sauya ranar soma jarrabawar bana

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne a cikin motar da ke dakon wasu manyan jami’an gwamnati, ciki har da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, yayin da suke kan hanyar zuwa naɗin sarauta da kuma ɗaurin auren ’yar tsohon gwamnan jihar, Muhammad Abdullahi Abubakar SAN.

Aminiya ta ruwaito cewa, a Juma’ar da ta gabata ce manyan jami’an gwamnati suka halarci ɗaurin auren Khadija Muhammad, da kuma naɗin sarautar Makama Babba I da aka gudanar a Fadar Sarkin Bauchi.

Sai dai cikin wata sanarwar mayar da martani kakkausa kan lamarin, kakakin mataimakin gwamnan, Muslim Lawal, ya musanta labarin, yana mai nanata cewa ubangidansa mutum ne mai mutunci da kamala da ba zai taɓa tsoma kansa cikin irin wannan hauragiya ba.

Amma wani da abin ya faru kan idonsa kuma ya buƙaci a sakaya sunansa, ya shaida wa Aminiya cewa, Mataimakin Gwamnan ya fusata ne bayan Ministan Harkokin Wajen ya riƙa jifar Gwamna Bala Mohammed da kalamai marasa daɗi. Majiyar ta ce wannan ce ta sanya rikicin ya hautsine a cikin motar da ke dakon manyan jami’an gwamnatin zuwa Fadar Masarautar Bauchi. Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin Minista Yusuf Tuggar ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Sai dai ɗan gwamnan jihar, Shamsuddeen Bala Mohammed na daga cikin waɗanda suka yi farin ciki da faruwar lamarin wanda ya riƙa tashe a dandalin sada zumunta na X.

Cikin wata wallafa mai tashe da ɗan gwamnan ya ƙara yaɗawa, mai ɗauke da saƙon cewa, “Mataimakin Gwamna na farko da ya mari Minista a Bauchi. Mista Taka ka sha mari….” da sauran saƙonni makamancin wannan da suke tashe.

Ana iya tuna cewa, wannan tsamin dangantaka ya samo asali ne tun bayan da Gwamna Bala Mohammed ya riƙa sukar Shugaba Bola Tinubu kan rashin shugabanci nagari.

A cewar gwamnan, manufofin da gwamnatin Tinubu ta ƙaƙaba sun jefa al’ummar ƙasar nan cikin ƙangin talauci da tsadar rayuwa.

Sai dai a martanin da Ministan ya mayar, ya ce gwamnan na fakewa da manufofin Tinubu domin ɓoye gazawarsa da zummar samun karɓuwa wajen neman kujerar shugabancin Nijeriya a Zaɓen 2027.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da ake zargin cewa shi kansa Ministan na fafutikar zama Gwamnan Bauchi a 2027.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ango ya tsere tare da surukarsa
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • Mayaƙan ISWAP sun tarwatsa gada a Yobe
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
  • Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?
  • Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa: Makiya Suna Adawa Da Fadada Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce: Iran Da Saudiyya Za Su Iya Magance Yawancin Matsalolin Yankin Gabas Ta Tsakiya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Za A Gudanar Da Zagaye Na Biyu Na Tattaunawar Iran Da Amurka A Birnin Roma Ne