Aminiya:
2025-02-28@21:53:38 GMT

Gwamnatin Sakkwato ta nemi malaman Jami’a su janye yajin aiki 

Published: 28th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Sakkwato, ta buƙaci malaman jami’ar jihar da suka shiga yajin aiki da su koma bakin aiki don ci gaban ilimi a jihar.

Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi, Farfesa Isah Muhammad Maishanu ne, ya bayyana haka a taron manema labarai da ya kira a ranar Juma’a, kwana ɗaya bayan da malaman suka fara yajin aiki saboda rashin biyansu haƙƙoƙinsu.

An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya  Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara

Ya ce: “Muna kira ga malaman da su sake tunani kan matakin da suka dauka. Kada su bari siyasa ko wasu da ba su da kishin jiha su yi amfani da su wajen hana ci gaban ilimi.

“Mu na mutunta su, kuma muna fatan su koma bakin aikinsu.”

Ya ƙara da cewa gwamnati ta ɗauki ƙorafe-ƙorafen malaman da muhimmanci, don haka an kafa kwamiti da ke tattaunawa da ɓangarorin da abin ya shafa kan matsalar rashin biyan su kaso 25 da 35 na albashinsu.

Dangane da matsalar gidajen malamai da suka fara lalacewa, kwamishinan ya bayyana cewa gwamnati ta tura injiniyoyi domin tantance halin da suke ciki da nufin gyara su.

Duk da haka, wasu masu sharhi a Sakkwato na ganin cewa gwamnati ba ta ɗauki matakan da suka dace don warware matsalar malaman ba.

A cewarsu, maimakon ɗaukar matakin magance matsalolin, gwamnati kawai tana bayar da umarni ne wanda ba ya taimakawa wajen yin sulhu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Janye Bincike Kan Shigo Da Jan Karfe

Ma’aikatar harkokin cinikayya ta kasar Sin ta bukaci Amurka da ta gaggauta janye binciken sashe na 232 kan shigo da jan karfe kasarta, inda ta bayyana cewa, zargin da ake yi na cewa kasar Sin na amfani da tallafin gwamnati da karfin samar da hajoji fiye da kima don gurgunta abokan takara kwata-kwata ba ya da tushe.

Kakakin ma’aikatar He Yadong ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a lokacin da yake amsa tambaya kan matakin da Amurka ta dauka na kaddamar da binciken sashe na 232 kan jan karfe da aka shigar da su kasar daga kasashen waje.

Ya kara da cewa, binciken na Amurka wani aiki ne na kashin kai da kariyar cinikayya wanda ta yi bisa fakewa da “tsaron kasa”, kuma matakin zai kara yin illa ga tsarin cinikayyar bangarori daban daban da kuma kawo cikas ga daidaiton tsarin samarwa, da rarraba hajoji tsakanin sassan kasa da kasa.

Kakakin ya ce, idan Amurka ta nace kan sanya karin haraji da sauran matakan takaitawa, Sin za ta dauki dukkan matakan da suka dace don kiyaye hakkoki da moriyarta. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Janye Bincike Kan Shigo Da Jan Karfe
  • Gwamnatin Kano ta nemi Tinubu ya kori Aminu Bayero daga fadar Nassarawa
  • A Karon Farko, Malaman Jami’ar Sakkwato Sun Tsunduma Yajin Aiki
  • Malaman Jami’ar Sakkwato sun tsunduma yajin aiki
  • Gwamnatin Kwara Ta Kaddamar Da Kwas Ga Dalibai Makarantun 50
  • Gwamna Namadi Ya Nada Jami’an Alhazai 27 Tare Da Kara Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
  • Gwamnatin Jigawa Ta Biya  Sama Da Naira Miliyan 730 Ga Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙaddamar Da Shirin Tallafin Abinci Na Naira Biliyan 4
  • Jami’an tsaro sun tarwatsa zanga-zangar da ta ɓarke a Kano