Aminiya:
2025-03-31@02:12:31 GMT

Gwamnatin Sakkwato ta nemi malaman Jami’a su janye yajin aiki 

Published: 28th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Sakkwato, ta buƙaci malaman jami’ar jihar da suka shiga yajin aiki da su koma bakin aiki don ci gaban ilimi a jihar.

Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi, Farfesa Isah Muhammad Maishanu ne, ya bayyana haka a taron manema labarai da ya kira a ranar Juma’a, kwana ɗaya bayan da malaman suka fara yajin aiki saboda rashin biyansu haƙƙoƙinsu.

An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya  Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara

Ya ce: “Muna kira ga malaman da su sake tunani kan matakin da suka dauka. Kada su bari siyasa ko wasu da ba su da kishin jiha su yi amfani da su wajen hana ci gaban ilimi.

“Mu na mutunta su, kuma muna fatan su koma bakin aikinsu.”

Ya ƙara da cewa gwamnati ta ɗauki ƙorafe-ƙorafen malaman da muhimmanci, don haka an kafa kwamiti da ke tattaunawa da ɓangarorin da abin ya shafa kan matsalar rashin biyan su kaso 25 da 35 na albashinsu.

Dangane da matsalar gidajen malamai da suka fara lalacewa, kwamishinan ya bayyana cewa gwamnati ta tura injiniyoyi domin tantance halin da suke ciki da nufin gyara su.

Duk da haka, wasu masu sharhi a Sakkwato na ganin cewa gwamnati ba ta ɗauki matakan da suka dace don warware matsalar malaman ba.

A cewarsu, maimakon ɗaukar matakin magance matsalolin, gwamnati kawai tana bayar da umarni ne wanda ba ya taimakawa wajen yin sulhu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su

Mai martaba Sarkin zazzau,kuma shugaban majalisar sarakunan jihar kaduna, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya bukaci Dagatan da ke masarautar zazzau da su rinka sanya ido sosai akan zirga-zirgar bakin fuskokin da ba su gane ba a cikin su.

Ya yi kiran ne a sakon sa na sallah bayan kammala azumin watan Ramadan a fadar sa dake Zaria.

Ahmed Nuhu Bamalli ya bayyana cewa harkar tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a hakki ne na kowa amma ba gwamnati ita kadai ba,a don haka akwai bukatar ganin an hada karfi da karfe domin samun nasara a game da tsaron.

Mai martaba Sarkin ya kuma bukaci Dagatan da su rinka kai rahoton zuwan duk wani bako ko bakuwa da kuma dalilin zuwan.

Ya ce idan har aka dauki wannan matakin matsalar tsaro za ta ragu sosai,yana mai nuni da cewa sarakunan gargajiya na da muhimman rawar da za su taka game da tsaro.

Haka kuma Sarkin na zazzau ya bukaci iyaye da su rinka sanya ido game da harkokin yau da kullum na ‘ya’yan su.

Haka kuma ya gode wa gwamnan jihar kaduna da shugaban majalisar wakilai,Dr Abbas Tajuddeen, Iyan zazzau saboda irin aiyukan ci gaban da suke samar wa talakawa a zaria da sauran kananan hukumomin jihar kaduna.

A wani labarin kuma,Limamin masallacin juma’a na rukunin kananan gidajen dake kofar Gayan,Zaria, Sheikh Dalhatu Bello Amaru ya yi Allah wadai da kisar Gilla da wasu yan ta’adda suka yi wa wasu mafarauta yan arewa su 11 a Uromi da ke jihar Edo.

Ya yi Allah wadan ne a hudubar sa ta sallar idin karamar sallah da ya gudanar.

Ya ce mutanen Arewa ba su amince da kisar gillar da aka yi wa maharban ba gaira ba dalili.

Sheikh Bello Amaru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihar Edo da su tabbatar da ganin an kamo duk mutanen da suka aikata laifin domin suma a kashe su domin ran su bai fi na mafarautar da suka kashe ba tare da wani dalili ba.

Ya yi Bayanin cewa Allah ya bada umurnin cewa duk wanda ya kashe wani shima a kashe shi,amma hakan bai bada damar wani ya dsuki doka a hannun shi ba,hakki ne na hukumomin da abin ya shafa.

Haliru Hamza

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi
  • ‘Yan Hamayyar Siyasar A Kasar Turkiya Suna Ci Gaba Da Yin Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne
  • Gwamnati Ta Ba da Umarnin Tafiya Yi Wa Ƙasa Hidima Ga Duk Masu HND
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba
  • Sallah: Hadimin gwamnan Sakkwato ya bai wa magoya bayan APC kyautar N22m
  • Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya