Aminiya:
2025-04-21@06:49:16 GMT

Gwamnatin Sakkwato ta nemi malaman Jami’a su janye yajin aiki 

Published: 28th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Sakkwato, ta buƙaci malaman jami’ar jihar da suka shiga yajin aiki da su koma bakin aiki don ci gaban ilimi a jihar.

Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi, Farfesa Isah Muhammad Maishanu ne, ya bayyana haka a taron manema labarai da ya kira a ranar Juma’a, kwana ɗaya bayan da malaman suka fara yajin aiki saboda rashin biyansu haƙƙoƙinsu.

An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya  Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara

Ya ce: “Muna kira ga malaman da su sake tunani kan matakin da suka dauka. Kada su bari siyasa ko wasu da ba su da kishin jiha su yi amfani da su wajen hana ci gaban ilimi.

“Mu na mutunta su, kuma muna fatan su koma bakin aikinsu.”

Ya ƙara da cewa gwamnati ta ɗauki ƙorafe-ƙorafen malaman da muhimmanci, don haka an kafa kwamiti da ke tattaunawa da ɓangarorin da abin ya shafa kan matsalar rashin biyan su kaso 25 da 35 na albashinsu.

Dangane da matsalar gidajen malamai da suka fara lalacewa, kwamishinan ya bayyana cewa gwamnati ta tura injiniyoyi domin tantance halin da suke ciki da nufin gyara su.

Duk da haka, wasu masu sharhi a Sakkwato na ganin cewa gwamnati ba ta ɗauki matakan da suka dace don warware matsalar malaman ba.

A cewarsu, maimakon ɗaukar matakin magance matsalolin, gwamnati kawai tana bayar da umarni ne wanda ba ya taimakawa wajen yin sulhu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhi:  Kalankuwar  Kona Rayayyu Da Wuta A Gaza
  • An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna
  • Amurka : Ana ci gaba da zanga-zangar kyamar tsare -tsare da manufofin gwamnatin Trump
  • Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
  • Manyan jami’an gwamnati sun halarci auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi
  • Yadda Za Ku Hada ‘Mimi Fankek’
  • Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (2)
  • Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki
  • Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC