Gobe Asabar 1 Ga Watan Ramadan 1446
Published: 28th, February 2025 GMT
Fadar mai alfarma sarkin Musulmi, ta sanar da ganin jinjirin watan Ramadan da maraicen Juma’ar nan a Sakkwato.
Cikin wata sanarwa da Mai Alfarma Sarkin Musulmin, Sa’ad Abubakar lll ya karanta a fadarsa, ya ce an ga watan a sassan ƙasar daban-daban.
Don haka ne ya ayyana ranar Asabar 1 ga watan Maris a matsayin 1 ga watan Ramadan 1446.
Nasiru Malami/Sakkwato
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
A Karon Farko, Malaman Jami’ar Sakkwato Sun Tsunduma Yajin Aiki
Kazalika sun yi ƙorafi tare da nuna rashin gamsuwa da yadda gwamnati da majalisar gudanarwar Jami’ar ke tafiyar da al’amuran da suka shafi ci gabanta.
Ƙungiyar malaman ta ce ta kafa wani kwamiti da zai tilasta tare da tabbatar da an bi umarnin yajin aikin da tsayawar harkoki a Jami’ar har sai an cimma matsaya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp