Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
Published: 28th, February 2025 GMT
Shuwagabannin Afrika ta Kudu, Malasiya da kuma Colombia sun jaddada matsayinsu nah ana jiragen ruwa dauke da makamai zuwa HKI tsayawa a tashishin jiragen Ruwan kasashen su.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ta nakalto shugaban Afirka ta kudu, Cyril Ramaphosa, Firaiministan kasar Malasiya Anwar Ibrahim da Shugaban kasar Colmbia Gustavo Petro suna fadar haka a wani rubutun hadin guiwa da aka buga a mujallar ‘Foreign Policy’ na wannan makon.
Shuwagabannin sun bayyana cewa yakin da HKI ta durawa Falasdinawa a Gaza, ya nuna yadda tsarin dokokin kasa da kasa suna gaza tabbatar da adalci a duniya.
Labarin ya kara da cewa : Ko mu hada kai mu tabbatar da dokokin kasa da kasa, ko kuma dukkan tsaron ya rushe.
Sun HKI ta aikata laifukan yaki a Gaza wadanda suka hada shafi al-umma a doron kasa, inda a cikin shekara guda ta kashe mutane kimani 61,000 tare da taimakon manya-manyan kasashen duniya ko kasashen yamma.
Kasashen Malasiya da Colombia dai suna cikin kasashen da suke goyon bayan karar da Afirka ta kudu da shigar kan HKI a kotun ICC, kuma ya zuwa yanzu kotun ta fidda sammacin kama shuwagabnnin HKI biyu, Wato Firay ministan kasar Benyamin Natanyaho da kuma tsohon ministan yakinsa Aut Galant.
Har’ila yau rubutun shuwagabannin uku ya yi tir da manufan shugaban kasar Amurka ta kwace Gaza ko kuma korar Falasdinawa daga kasarsu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya
Asbitin ‘Mount Sinai’ (Dotsen Sinaa’ a kasar Amurka ta salami wata likita daga aiki, bayan da aika da wani rubutu da hoto a shafukan yanar gizo tana, wanda Asbitin tana cewa ai Musanta hare-haren ranar 7th ga watan Octoba ne’.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta bayyana cewa Dr Leila Abbasi,diyar shekara 46 a duniya, ta aika sako cikin shafinta na yanar gizo inda take goyon bayan kungiyoyin Hamas da Hizbullah na kasar Lebanon sannan tana allawadai da kuma aibata HKI kan kissan yara da take yi a Gaza.
Gwamnatin kasar Amurka dai tana ganin kanta a matsayin kasa wacce take gaba wajen kare hakkin fadin albarkacin baki, amma idan al-amarin ya shafi HKI sai ta nuna fuska biyu. Ta kuma kareta ido a rufe kamar sauran Amurkawa da kuma kasashen duniya basa kallo.
Tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 zuwa yanzu sojojin HKI ta kashe falasdinawa akalla dubu 50 a gaza kashi 2/3 daga cikinsu mata da yara ne.
Sannan abin ya yi muni inda gwamnatin Amurka ta tsaya gaban kotun ICC wacce ta tabbatar da laifukan HKI, ta kuma bada sammacin kama Firai ministan HKI da tsohon ministan yakin sa Yoav Galant. Inda ta kakabawa jami’an kotun takunkuman tattalin arziki.