Shuwagabannin Afrika ta Kudu, Malasiya da kuma Colombia sun jaddada matsayinsu nah ana jiragen ruwa dauke da makamai zuwa HKI tsayawa a tashishin jiragen Ruwan kasashen su.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ta nakalto shugaban Afirka ta kudu, Cyril Ramaphosa, Firaiministan kasar Malasiya Anwar Ibrahim da Shugaban kasar Colmbia Gustavo Petro suna fadar haka a wani rubutun hadin guiwa da aka buga a mujallar ‘Foreign Policy’ na wannan makon.

Shuwagabannin sun bayyana cewa yakin da HKI ta durawa Falasdinawa a Gaza, ya nuna yadda tsarin dokokin kasa da kasa suna gaza tabbatar da adalci a duniya.

Labarin ya kara da cewa : Ko mu hada kai mu tabbatar da dokokin kasa da kasa, ko kuma dukkan tsaron ya rushe.

Sun HKI ta aikata laifukan yaki a Gaza wadanda suka hada shafi al-umma a doron kasa, inda a cikin shekara guda ta kashe mutane kimani 61,000 tare da taimakon manya-manyan kasashen duniya ko kasashen yamma.

Kasashen Malasiya da Colombia dai suna cikin kasashen da suke goyon bayan karar da Afirka ta kudu da shigar kan HKI a kotun ICC, kuma ya zuwa yanzu kotun ta fidda sammacin kama shuwagabnnin HKI biyu, Wato Firay ministan kasar Benyamin Natanyaho da kuma tsohon ministan yakinsa Aut Galant.

Har’ila yau rubutun shuwagabannin uku ya yi tir da manufan shugaban kasar Amurka ta kwace Gaza ko kuma korar Falasdinawa daga kasarsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Mujalla Ta Zabi Shugaban NPA A Matsayin Gwarzonta Na Shekarar 2025

“A karkashin Shugabancin Dantsoho, ya taimaka wajen ganin ana sauke sundukan kayan da aka yo jigilarsu a cikin sauki, musamman a Tashar Lekki wanda hakan ya taimaka, wajen rage cunkso a Tashar.” A cewar Mahukuntan Mullar.

Mahukuntan Mullar sun kara da cewa, sun zabo Dantso ne, ganin cewa, shi ne, na farko da aka zaba a mukamin Shugaba na Kungiyar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Gabas da yankin Afirka ta Tsakiya PMAWCA, inda zabarsa, ta kara daga kima da darajar Nijeriya, a fannin harkokin tafiyar da Tashohin Jiragen Ruwa, a yankin.

A yayin da yake karbar babbar lambar yabon Mullar Dakta Dantsoho ya bayar da tabbacin cewa, zai kara zage damtse wajen shugabantar Hukumar, daidai da tsare-tsaren Miniatan bunkasa tattalin arzki na Teku Adegboyega Oyetola, musaman domin Hukumar ta kara dorawa, kan nasarorin da ta zamar, ya zuwa yanzu.

Dantso ya kuma bai wa masu ruwa da tsaki a Hukumar ta NPA, tabbacin ci gaba da zuba duk wata kwarewa da yake da ita, domin a kara habaka tattalin arzikin kasar.

Ya sanar da cewa, lambar yabon, za ta karawa Hukumar karsashi wajen kara jajirewa na kara samar da damar hada-hadar kasuwanci, a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • Kwastam Da Hukumar NPA Sun Kulla Hadakar Bunkasa Ingancin Aiki A Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Wata Mujalla Ta Zabi Shugaban NPA A Matsayin Gwarzonta Na Shekarar 2025
  • Pezeshkian: Wajibi Ne Kasashen Musulmi Su Kara Karfafa Alakokinsu
  • Habasha Da Somaliya Sun Cimma Yarjeniyoyin Fahimtar Juna A Tsakaninsu
  • Masar Ta Yi Watsi Da Shawarar Cewa Ta Karbi Ragamar Gaza Na Wucin Gadi
  • Jami’an Diblomasiyyar Kasashen Rasha Da Amurka Zasu Sake Haduwa A Birnin Istambul A Gobe
  • Wakilin Sin: Dole Ne A Aiwatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Shugabannin Afirka Ta Kudu, Malaysia Da Colombia Sun Yi Kira Da A Kawo Karshen Laifukan Isra’ila