An Yi Jana’izar Shahidan kungiyar Hizbullah Fiye Da 120 Kudancin Kasar Lebanon A Yau Jumma’a
Published: 28th, February 2025 GMT
Shadidan Hizbullah kimabi 130 ne aka yi jana’izarsu a yau jumma’a a kudancin kasar Lebanon. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran tanakalto kungiyar Hizbullah na fadar haka, ya kuma kara da cewa kungiyar ta gabatar da shihidar da dama saboda kare kasarsu, saboda kare kasar Lebanon daga mamayar HKI.
Labarin ya kara da cewa an gudanar da jana’izar ne a garuruwan Aitarun da kuma Aita shaab. Inda mutanen da dam dagayankin zuka halarta . Labarin ya kara da cewa Shahidan sun kai ga shahada ne a hare-haren da sojojin HKI suka kai kan kudancin kasar ta Lebanon a cikin watannin Octoba da kuma Nuwamba na shekara ta 2024.
Labarin ya kara da cewa a yakin dai mutanen leabin kimani 4000 ne suka rasa rayukansu mafi yawansu fararen hula ne wadanda basu san hawa ko sauka ba.
Kafin jana’izar yau ma, sojojin HKI da suke mamaye da wasu wurare a kudancin kasar Lebanon sun yi harbi da bindiga don tsoratar da mutane masu Jana’izar, wanda hakan ya kasance keta yarjeniyar da aka kulla da Ita
A dai dai lokacin ne sojojin HKI ta kashe manya-manyan shuwagabanni da kwamandojojin sojojin Hizbullah na kasar wanda ya hada har da shugaban kungiyar Sayyid Hassan Nasarallah, da magajinsa Sayyid Hashin Safiyyuddiin, wadanda aka yi masu jana’iza a ranakin 23-24 na watan fabarairu da muke ciki a birnin Neirut babban birnin kasar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Lebanon kara da cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
Rundunar sojin Amurka ta kaddamar da wani hari ta sama a ranar Asabar din da ta gabata kan mayakan IS a yankin Puntland na Somalia, inda suka kashe wasu mambobin kungiyar da dama, a cewar rundunar sojin Amurka .
A cikin wata sanarwa da ta fitar, rundunar sojin Amurka da ke nahiyar Turai ta tabbatar da cewa, harin da aka kai tare da hadin gwiwar gwamnatin Somaliya, ya kashe da dama na mayakan ISIS a Somaliya.
Yayin da kungiyar IS ke hankoro hada karfinta a Somalia wanda bai bunkasa ba idan aka kwatanta da kungiyar Al-Shabaab mai alaka da Al-Qaeda, kungiyar ta mayar da hankalinta ne wajen kara fadada karfinta a yankin Puntland mai cin gashin kansa.
“Harin ya auke ne a kudu maso gabashin Bosasso, Puntland, a arewa maso gabashin Somalia,” in ji sanarwar.
Wannan farmakin ya biyo bayan wani harin makamancin haka ne kwanaki biyu da suka gabata, wanda AFRICOM ta bayyana a matsayin wani babban shiri na yaki da ta’addanci a Somaliya.
A cikin watan Fabrairu, hare-haren da Amurka ta kai kan kungiyar IS a Puntland, hukumomin yankin sun bayar da rahoton cewa an kashe “muhimman mutane”, ko da yake ba su bayar da karin bayani ba.
A wani mataki na kare martabar yankinta da kuma ja da baya kan rarrabuwar kawuna, rahotanni sun ce Somaliya ta bai wa Amurka damar iko kan muhimman tashoshin jiragen ruwa da sansanonin jiragen sama dake Somaliland da Puntland.