Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta ‘Euro-Med Monitor’ Ta Ce Ta Sami Shaidu Wadanda Suka Tabbatar Da Cewa HKI Tana Azabtar Da Fulasdinwa
Published: 28th, February 2025 GMT
Wata kungiyar kare hakkin bil’adama mai zaman kanta wacce take da cibiya a birnin Geneva na kasar Swizlanta ta bada sanarwan cewa ta sami cikekken shaidu wadanda suke tabbatar da cewa gwamnatin HKI tana azabtar da falasdinawa wadanda take tsare da su.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar tana bada wannan sanarwan a jiya Alhamis, ta kuma kara da cewa Jami’an gidajen yari da kuma sojjin HKI suna dukan kawo wuka kan falasdinawa da suka shiga hannunsu, sannan suna azabtar da su sosai, daga ciki har tare da yanke yanke wasu gabban jikinsu.
Kungiyar ta kara da cewa, mutum yana iya ganin alamun duka da kuma kumburan wurare da dama a jikin Falasdiwa.
Banda haka Falasdinawan da aka saka, sun bayyana cewa bayan duka da kuma azabtarwa sojojin HKI sukan hana magunguna ga wadanda basa da lafiya har wasunsu su rasa rayukansu.
Rahoton ya kara da cewa wadannan shaidun sun tabbatar da cewa, HKI tana aikata laifukan yaki, a kan al-ummar Falasdinu sannan alamu sun nuna cewa Falasdinawa da dama sun rasa rayukansu a gidajen yari k kuma wauraren da yahudawan suke tsare da su. Sannan HKI tana buye duk wata shaida da suke tabbatar da irin mummunar mu’amalan da suke yi da Falasdinawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba
Shugaban majalisar mulkin kasar Sudan kuma kwamandan Sojin kasar Abdel Fattah al-Burhan ya tabbatar da cewa, farin cikin samun nasara a Sudan ba zai cika ba har sai an kawar da tungar karshe ta mayakan RSF a kasar, yana mai jaddada cewa kasar ba za ta ja da baya ba har sai an murkushe wadannan mayakan ‘yan tawaye, wadanda suka aikata munanan laifuka kan al’ummar Sudan.
Al-Burhan ya yi nuni da cewa, za a ci gaba da gwabzawa har sai an samu cikakken adalci, yayin da ya tabbatar da cewa ya tsaya tsayin daka da dukkan ‘yan kasar, kuma ya yi imani da ci gaba da kokarin maido da tsaro da kwanciyar hankali a kowane sako na kasar Sudan.
Al-Burhan ya ce: Har yanzu hanyar zaman lafiya da kawo karshen yakin a bude take, kuma duk wannan abu ne mai yiyuwa, kuma hanya a fili take, wato kungiyar RSF ta ajiye makamanta.
Ya tabbatar da cewa babu wata niyya ta tattaunawa da Rundunar ta RSF a yanzu, inda ya bayyana cewa kofar yin afuwa a bude take ga duk wanda ya ajiye makamansa. A ranar Asabar din da ta gabata ce sojojin kasar Sudan suka sake karbe ikon Kasuwar Libiya da ke yammacin birnin Omdurman, lamarin da ke nuna wani gagarumin mataki na ci gaba da suke samu, wanda ya biyo bayan sake kwac fadar shugaban kasa daga hannun dakarun RSF da sojojin na Sudan suka yi.