Wata kungiyar kare hakkin bil’adama mai zaman kanta wacce take da cibiya a birnin Geneva na kasar Swizlanta ta bada sanarwan cewa ta sami cikekken shaidu wadanda suke tabbatar da cewa gwamnatin HKI tana azabtar da falasdinawa wadanda take tsare da su.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar tana bada wannan sanarwan a jiya Alhamis, ta kuma kara da cewa Jami’an gidajen yari da kuma sojjin HKI suna dukan kawo wuka kan falasdinawa da suka shiga hannunsu, sannan suna azabtar da su sosai, daga ciki har tare da yanke yanke wasu gabban jikinsu.

Kungiyar ta kara da cewa, mutum yana iya ganin alamun duka da kuma kumburan wurare da dama a jikin Falasdiwa.

Banda haka Falasdinawan da aka saka, sun bayyana cewa bayan duka da kuma azabtarwa sojojin HKI sukan hana magunguna ga wadanda basa da lafiya har wasunsu su rasa rayukansu.

Rahoton ya kara da cewa wadannan shaidun sun tabbatar da cewa, HKI tana aikata laifukan yaki, a kan al-ummar Falasdinu sannan alamu sun nuna cewa Falasdinawa da dama sun rasa rayukansu a gidajen yari k kuma wauraren da yahudawan suke tsare da su. Sannan HKI tana buye duk wata shaida da suke tabbatar da irin mummunar mu’amalan da suke yi da Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara

Dakarun Sojin ‘Operation FANSAN YANMA’, sun kama Ƙasurgumin Shugaban ’Yan Bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu, wanda ya addabi al’ummar Mada, Tsafe, da wasu yankunan Jihar Zamfara.

Dakarun sun kai farmaki Hegin Mahe, Ruwan Bore, garin Mada, a Ƙaramar Hukumar Gusau a ranar 27 ga watan Fabrairu.

Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano

Bayan musayar wuta, sojoji sun kashe wasu ’yan bindiga, yayin da Nabamamu ya tsere zuwa cikin wani gida, amma daga ƙarshe dakarun suka cafke shi.

Bayan kama shi, ɗaya daga cikin yaransa, Bakin Malam, ya jagoranci kai harin ramuwar gayya wasu ƙauyuka, wanda ya tilasta wa mazauna ƙauyukan tserewa.

Sai dai dakarun sun mayar da martani, inda suka fatattaki ’yan bindigar, tare da ƙara jibge sojoji don tabbatar da tsaro a yankin.

Nabamamu, ya kasance almajiri ne, daga baya ya zama hatsabibin ɗan bindiga wanda ya yi sanadin ajalin mutane masu yawan gaske.

Ya jagoranci sama da mayaƙa 100, inda yake karɓar haraji daga hannun mazauna wasu ƙauyuka, kuma yana da alaƙa da masu yi wa wasu mahara safarar makamai a yankin.

Kama shi na iya rage ƙarfin ’yan bindiga a Zamfara, yayin da sojoji ke ƙara ƙaimi domin kawar da barazanar tsaro da tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara
  • Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa
  • LEADERSHIP HAUSA Ta Bayyana Wadanda Suka Yi Nasara A Gasar Gajerun Labaran Soyayya
  • Gwamnatin Jigawa Ta Biya  Sama Da Naira Miliyan 730 Ga Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya
  • Sheikh Na’im Kasim Ya Gana Da Ministan Harkokin wajen Kasar Iran Da Shugaban Majalisar Dokoki
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Biya Diyar Sama Da N1.5 Biliyan Ga Wadanda Aikin Tituna Ya Shafa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Biya Diyar Sama Da Naira Biliyan 5 Ga Wadanda Aikin Tituna Ya Shafa
  •                           Me Turkiya Take So A Syria?