Wata kungiyar kare hakkin bil’adama mai zaman kanta wacce take da cibiya a birnin Geneva na kasar Swizlanta ta bada sanarwan cewa ta sami cikekken shaidu wadanda suke tabbatar da cewa gwamnatin HKI tana azabtar da falasdinawa wadanda take tsare da su.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar tana bada wannan sanarwan a jiya Alhamis, ta kuma kara da cewa Jami’an gidajen yari da kuma sojjin HKI suna dukan kawo wuka kan falasdinawa da suka shiga hannunsu, sannan suna azabtar da su sosai, daga ciki har tare da yanke yanke wasu gabban jikinsu.

Kungiyar ta kara da cewa, mutum yana iya ganin alamun duka da kuma kumburan wurare da dama a jikin Falasdiwa.

Banda haka Falasdinawan da aka saka, sun bayyana cewa bayan duka da kuma azabtarwa sojojin HKI sukan hana magunguna ga wadanda basa da lafiya har wasunsu su rasa rayukansu.

Rahoton ya kara da cewa wadannan shaidun sun tabbatar da cewa, HKI tana aikata laifukan yaki, a kan al-ummar Falasdinu sannan alamu sun nuna cewa Falasdinawa da dama sun rasa rayukansu a gidajen yari k kuma wauraren da yahudawan suke tsare da su. Sannan HKI tana buye duk wata shaida da suke tabbatar da irin mummunar mu’amalan da suke yi da Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia

Rundunar ’yan sandan Jihar Benuwe a ranar Alhamis ta tabbatar da cewa an samu kwanciyar hankali a unguwar Otobi da ke Ƙaramar hukumar Otukpo biyo bayan wani mummunan hari da ya tilastawa mazauna garin barin gidajensu.

Kakakin rundunar ’yan sandan, CSP Catherine Anene a wata tattaunawa ta wayar tarho da wakiliyarmu, ta kuma yi watsi da rahoton sabbin hare-haren da aka kai kan unguwannin Emichi, Okpomaju da Odudaje, inda ta bayyana su a matsayin rahoton ƙarya don yawo tsoratar da jama’a.

An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno ’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista

“Unguwar Otobi yanzu akwai kwanciyar hankali, mun bar wasu jami’anmu tun ranar Laraba ana gudanar da bincike,” in ji Anene.

A halin da ake ciki, Gwamnan Jihar Benuwe, Hyacinth Alia ya bayyana cewa har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyen ba bayan harin.

“Mun yi asarar mutane 11. Mun tura ƙarin jami’an tsaro,” in ji gwamnan yayin wani taron manema labarai inda ya bayyana hare-haren a matsayin batun ƙwace fili.”

Da yake mayar da martani kan wannan ci gaban, Sanata mai wakiltar mazaɓar Benuwe ta Kudu kuma shugaban marasa rinjaye na Majalisar Dattawa, Abba Moro ya yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta ci gaba da gazawa wajen kare rayuka, al’ummarsa za su iya amfani da hanyoyin kare kansu.

Sanatan, a cikin wata sanarwa da Emmanuel Eche’Ofun John, mashawarcinsa kan harkokin yaɗa labarai ya fitar, ya bayyana cewa hare-haren da suka janyo asarar rayuka da dukiyoyi na biliyoyin Naira abu ne da ba za a amince da su ba.

Ya kuma yi kira ga gwamnatoci a kowane mataki da su tashi tsaye wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ya kuma yabawa Gwamna Alia da a ƙarshe ya fito ya yi Allah-wadai da wannan aika-aika a jihar, ya kuma buƙace shi da ya ƙara yi wa al’umma aiki, yana mai jaddada cewa ƙoƙarin gwamnati a dukkan matakai bai isa ba.

Moro ya kuma yi kira da a kafa sansanonin hukumomin tsaro a cikin unguwannin jama’a masu rauni

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna
  • Fursunoni 9 Sun Tsere Daga Gidan Gyara Hali A Jihar Kwara, An Cafko Guda Daya
  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • Rugujewar Gini A Legas: Adadin wadanda Suka Mutu Ya Kai Biyar, An Ceto 20
  • Kasar Rasha Ta Sanar Da Tsagaita Bude Wuta Da Ukraine Na Tsawon Kwanaki Bikin Ester
  • Amurka ta sanar da cewa za ta rage yawan sojojinta a Syria da rabi
  • An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a Neja
  • Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia
  • Amurka Ta Kashe Mutane 38 Tare Da Jikkata Fiye Da 100 A Harin Da Ta Kai Lardin Al-Hudaidah Na Yemen
  • Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.