Hukumar Lamuni Ta Duniya IMF Da Bankin Duniya Sun Ce Bazasu Taimakawa Lebanon Ba Sai Da Sharudda
Published: 28th, February 2025 GMT
Hukumar bada lamuni ta Duniya IMF da kuma bankin duniya, manya-manyan cibiyoyin kudade a duniya sun ce ba zasu bada kudade don sake gina kasar Lebanon ba, sai sun cika wasu sharudda zuwa wani lokaci. Kuma sune samar da huldar jakadanci da HKI da kuma kwance damarar kungiyar Hizbullah.
Jaridar Al-Akhbar ta kasar Lebanon ta nakalto shugaban hukumar IMF Kristalina Georgieva ta fadawa gwamnan babban bankin kasar Lebanon na riko, Wassim Mansouri a wata haduwa da suka y ikan cewa kasarsa zata sami kudaden sake gidan kasar dag wajenta ne, tare da sharudda.
Rahoton ya kara da cewa kasashen Lebanon da Siriya zasu sami kudade daga cibiyoyin biyu ne kawaii dan sun samar da dangantakar diblomasiyya da HKI. Sannan kasar Lebanon kuma sai ta hada da kwance damara, ko ta kwace makaman kungiyar Hizbullah ta kasar wacce take yakar HKI.
Kafin haka dai ministan kudi na kasar Lebanon Yassin Jabir yace bankin duniya ta warewa kasar Lebanon dalar Amurka billiyon daya don sake gina kasar Lebanon bayan yakin da kungiyar Hizbulla ta fafata da HKI.
Labarin ya kammala da cewa idan kasar Lebanon ta cika sharuddan da kasashen yamma suka shardanta zata sami kudaden a cikin watan Maris mai zuwa.
Haka ma kungiyar tarayyar Turai tana da sharudda nab awa kasar Lebanon Euro miliyon E500 saboda ta taimaka ta hana bakin haure shiga kasashen turai daga kasar.
Wasu kafafen yada labarai a kasar Lebanon sun bayyana cewa kasar tana bukatar dalar Amurka biliyon biliyon 6-7 don sake gida abubuwan da HKI ta lalata a yankin da ta yi da kungiyar Hizbullah a shekara ta 2023-2024.
HKI ta amince da tsagaita wuta a dole bayan da mayakan hizbullah sun yi mata barna mai yawa a yakin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara
Rundunar ’yan sandan Jihar Zamfara ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake kira Ɗan Mudale da ya addabi mazauna yankin Tsafe da kewaye.
Rundunar ta ce a jiya Alhamis ne ta daƙile wani harin ’yan bindiga a ƙauyen Keta da ke Ƙaramar Hukumar Tsafe ta jihar.
’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano Ɓarayin kekunan ɗinki sun shiga hannu a BornoHakan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Yazid Abubakar ya fitar a Gusau, babban birnin jihar.
A cewar DSP Yazid, a yayin daƙile harin ne ’yan sanda suka kashe gomman ’yan bindigar ciki har da Ɗan Mudale wanda ya addabi al’ummar yankin.
Ya ce rundunar haɗin gwiwa da ta haɗa da ’yan sanda da askarawa da kuma mafarauta ce ta yi karon batta da ’yan ta’addar da aka riƙa musayar wuta.
Sai dai ya bayyana takaicin cewa wani jami’in ɗan sanda daya da askarawa huɗu da kuma mafarauta sun bayar da ransu a yayin artabun.
Sanarwar ta ce a halin yanzu wasu mafarauta biyu na karɓar magani a Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Gusau.
Kazalika, rundunar ’yan sandan ta ƙara jaddada ƙudirinta na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
Ta yi kira ga mazauna da su riƙa gaggauta miƙa mata rahoton duk wani motsi da su aminta da shi ba domin a ɗauki matakin da ya dace.
Mutuwar Ɗan Mudale ne zuwa bayan kashe Kachalla Isuhu Yellow, wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ke sahun waɗanda suka jagoranci kitsa harin da aka kai jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja shekaru biyu da suka gabata.