Aminiya:
2025-03-31@06:30:36 GMT

Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano

Published: 28th, February 2025 GMT

Hukumar Karɓar Koke-Koke da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano (PCACC), ta kama Shugaban Ƙaramar Hukumar Ƙiru, Abdullahi Mohammed, bisa zargin sayar da filin da aka tanada don gina Filin Wasa na Kafin Maiyaki.

Ana zargin cewa Mohammed, ya sayar wa wani kamfani mai suna Mahasum filin.

An ga watan Ramadan a Najeriya An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya 

An gano cewar an tura kuɗin filin Naira miliyan 100 a asusun banki na shugaban.

Mai magana da yawun ƙaramar hukumar, Kabir Abba Kabir, ya tabbatar da kama Mohammed.

Ya tabbatar da cewa an tura jimillar kuɗi har Naira miliyan 240 tsakanin Nuwamba 2024 zuwa Fabrairu 2025, a asusunsa.

Sai dai hukumar ta ce ta karɓo kuɗaɗen haba ɗaya.

A cewar hukumar Mohammed, yana bayar da haɗin kai wajen binciken, yayin da hukumomi ke ƙoƙarin bankaɗo cikakkun bayanai game da badaƙalar.

Hukumar ta jaddada ƙudirinta na yaƙi da cin hanci da tabbatar da gaskiya a tafiyar da shugabanci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Badaƙalar Fili Ciyaman Ƙaramar Hukuma Ƙaramar Hukumar Ƙiru rashawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gobe Ta Ke Sallah A Nijeriya – Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, ya sanar da ganin jinjirin watan Shawwal a Nijeriya, kamar yadda kwamitin duban wata ya tabbatar.

Baya ga Nijeriya, ƙasashen Saudiyya, Bangladesh, da Indiya suma sun ga watan a yau, Asabar 29 ga watan Ramadan, 1446.

An Ga Watan Sallah A Ƙasar Saudiyya Abubuwan da Za ki Runguma domin Burge Mijinki

Sai dai wasu ƙasashe kamar Malaysia sun sanar da cewa za su yi Sallah ranar Litinin.

Hakan na nufin cewa azumin watan Ramadan ya ƙare, kuma al’ummar Musulmi a Nijeriya za su gudanar da bikin ƙaramar sallah gobe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane Biyu Sun Mutu, 20 Sun Jikkata A Yamutsin Filin Idi A Gombe
  • Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
  • Hotunan Sallar Idi daga sassan duniya
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Karrama Hakimai Da Limamai Da Kayan Sallah
  • Gobe Ta Ke Sallah A Nijeriya – Sarkin Musulmi
  • An Tabbatar Da Ganin Watan Shawwal A Nijeriya
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Bada Tallafin Noman Rani Ga Manoma 300
  • Wani Jami’in Leken Asirin HKI Ya Bukaci Kasashen Afirka Su Taimaka Su Karmi Falasdinawan Da Za;a Kora Daga Gaza
  • ’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano
  • An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa