Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano
Published: 28th, February 2025 GMT
Hukumar Karɓar Koke-Koke da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano (PCACC), ta kama Shugaban Ƙaramar Hukumar Ƙiru, Abdullahi Mohammed, bisa zargin sayar da filin da aka tanada don gina Filin Wasa na Kafin Maiyaki.
Ana zargin cewa Mohammed, ya sayar wa wani kamfani mai suna Mahasum filin.
An ga watan Ramadan a Najeriya An ga jinjirin watan Ramadan a SaudiyyaAn gano cewar an tura kuɗin filin Naira miliyan 100 a asusun banki na shugaban.
Mai magana da yawun ƙaramar hukumar, Kabir Abba Kabir, ya tabbatar da kama Mohammed.
Ya tabbatar da cewa an tura jimillar kuɗi har Naira miliyan 240 tsakanin Nuwamba 2024 zuwa Fabrairu 2025, a asusunsa.
Sai dai hukumar ta ce ta karɓo kuɗaɗen haba ɗaya.
A cewar hukumar Mohammed, yana bayar da haɗin kai wajen binciken, yayin da hukumomi ke ƙoƙarin bankaɗo cikakkun bayanai game da badaƙalar.
Hukumar ta jaddada ƙudirinta na yaƙi da cin hanci da tabbatar da gaskiya a tafiyar da shugabanci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Badaƙalar Fili Ciyaman Ƙaramar Hukuma Ƙaramar Hukumar Ƙiru rashawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Bincika Zargin Zaftare Albashin Ma’aikatan Gwamnati.
Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya yi wani kakkausan gargadi game da rahotannin rashin biyan albashi da rashin biyan ma’aikatan jihar, inda ya bayyana hakan a matsayin tauye hakkin ma’aikata da kuma cin amanar jama’a.
Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake kaddamar da kwamitin bincike mai mutane bakwai, karkashin jagorancin Hon. Abdulkadir Abdussalam, domin gano musabbabin sabanin.
Sakataren gwamnatin jiha Alhaji Umar Faruk ya wakilta, ya ce kwamitin ya hada da manyan jami’an gwamnati da masana harkokin kudi da wadanda suka kware a tsarin biyan albashi.
Yace Membobin Kwamitin sune Abdulkadir Abdussalam_ – Shugaban, Kwamishinan Karkara da Ci gaban Al’umma Dr. Bashir Abdu Muzakkari – memba, mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin dijital, Dr. Aliyu Isa Aliyu – Memba, Darakta-Janar na Ofishin Kididdiga na Jihar Kano.
Dokta Hamisu Sadi Ali, Memba, Babban Darakta Janar na Ofishin Kula da Bashi na Jihar Kano, Hajiya Zainab Abdulkadir – Mamba, Darakta, Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano, Aliyu Muhammad Sani – Sakatare, Darakta, Bincike da Aiki na Hukumar REPA, Ofishin SSG.
Ummulkulthum Ladan Kailani – zata kasance mataiamakiyar sakataren kwamitin.
Ya ce an baiwa kwamitin kwanaki bakwai don gabatar da cikakken rahoto.
Gwamnan ya kuma tabbatar wa da ma’aikatan gwamnati cewa gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da adalci, gaskiya da kuma biyan albashi cikin gaggawa, yana mai gargadin cewa duk wanda aka samu da laifin cin zarafin ma’aikata zai fuskanci mummunan sakamako.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO