Alkaluman da hukumar kididdga ta kasar Sin ta bayar a yau Jumma’a sun shaida cewa, yawan mutanen kasashen waje da suka shigo babban yankin kasar Sin ba tare da biza ba a bara, ya kai miliyan 20.12, adadin da ya karu da kaso 112.3%.

Bisa ga alkaluman, yawan baki masu yawon shakatawa da suka shigo babban yankin kasar a bara ya kai miliyan 131.

9, wanda ya karu da kaso 60.8%, kuma daga cikinsu miliyan 26.94 ’yan kasashen waje ne, sauran kuma sun fito daga yankunan Hong Kong da Macao da Taiwan na kasar Sin. Sa’an nan, kudin da baki masu yawon shakatawa suka kashe ya kai dala biliyan 94.2, wanda ya karu da kaso 77.8%. Ban da haka, yawan mazauna babban yankin kasar Sin da suka fita daga kasar ya kai miliyan 145.89, kuma daga cikinsu miliyan 97.12 sun je yankunan Hong Kong da Macao da Taiwan. (Lubabatu Lei)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

Kasar Sin ce ke da kusan kashi 30 cikin 100 na karuwar tattalin arzikin duniya a bara, wanda ya yi tasiri matuka ga tattalin arzikin duniya. Gudunmawar da kasar Sin ta bayar ta sake tabbatar da matsayinta na kan gaba a fannin tattalin arziki, kuma ta nuna muhimmiyar rawar da take takawa wajen ciyar da harkokin cinikayyar kasa da kasa gaba, da karfafa zuba jari da ingiza kirkire-kirkire na fasaha. Hakazalika, darajar cinikin waje na kasar Sin ta kai wani matsayi mafi girma a shekarar 2024, inda jimilarta ta kai yuan triliyan 43.85, wanda ya karu da kashi 5 cikin dari bisa na shekara 2023. Haka ma yawan kayayyakin da ake fitarwa zuwa kasashen waje ya karu da kashi 7.1 cikin dari idan aka kwatanta da na shekarar 2023 zuwa yuan tiriliyan 25.45 yayin da yawan kayayyaki da aka shigo da su ya karu da kashi 2.3 cikin dari zuwa yuan tiriliyan 18.39.

Hakazalika, Ci gaban kasar Sin yana haifar da tasiri a sassa da dama, ciki har da masana’antu, da fasaha da ayyuka. Tasirin ayyukanta da suka shafi tattalin arziki yana daidaita kasuwannin duniya, yana haifar da bukatun fitar da kayayyaki daga wasu kasashe, kuma yana taimakawa farfadowar tattalin arzikin yankunan da cutar ta COVID-19 ta fi shafa. Gudunmawar da kasar Sin ta bayar wajen samun ci gaban duniya a shekarar 2024 ta kara tabbatar da rawar da ta taka wajen farfadowa bayan barkewar annobar. Musamman ma, karuwar kayayyakin da kasar Sin ke shigowa da su daga kasashen waje, na taimakawa kasashe masu tasowa wajen habaka kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasashen waje, da gaggauta farfado da tattalin arzikinsu. Ta hanyar soke haraji kan kayayyakin da ke shigowa daga kasashe masu karancin ci gaba wadanda ke da huldar diflomasiyya da kasar Sin, kasar ta nuna aniyarta ta inganta ci gaban tattalin arzikin duniya, da zama amintacciyar abokiyar hulda a fannin tattalin arziki. Wannan manufar ba wai kawai tana karfafa huldar cinikayya da wadannan kasashe ba ne, har ma tana taimaka musu su shiga cikin kasuwannin duniya a dama da su, da samar da ci gaba mai dorewa da kuma taimakawa wajen rage talauci. Kasashe masu tasowa sun kasance babban jigon da ke ingiza fitar da kayayyaki daga kasar Sin zuwa kasashen waje, musamman kasashen da ke aikin samar da ababen more rayuwa karkashin tsarin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya. Hasali ma, a shekarar 2024, kasashen da ke cikin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya sun kai sama da kashi 50 cikin 100 na jimillar cinikin waje na kasar Sin a karon farko. Wannan ya nuna yadda shawarar Ziri Daya da Hanya Daya ke da girma wajen karfafa huldar cinikayya da hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin kasar Sin da sauran kasashe masu tasowa, tare da karfafa rawar da kasar ke takawa a fannin cinikayya da raya ababen more rayuwa a duniya. Kasar Sin ta kara fadada kasuwannin fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje a kasashe masu tasowa, tare da inganta cinikayya ta hanyar samun moriyar juna. Yayin da wadannan kasashe ke samun damar shiga kasuwannin kasar Sin mai matukar girma don samar da albarkatun kasa, jarin da kasar Sin ta zuba a fannin ababen more rayuwa karkashin tsarin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya na samar da muhimman damammakin ci gaba ga wadannan kasashe, da samar da ci gaban tattalin arziki da hada kai. Wannan hadin gwiwa ba wai kawai yana karfafa huldar kasuwanci ba, har ma yana sa kaimi ga ci gaba mai dorewa da hadin gwiwar tattalin arziki, tare da amfanar da kasar Sin da abokan huldar kasuwanci a kasashe masu tasowa.

Akwai Daidaito A Adadin Kayayyakin Da Sin Ke Fitarwa Zuwa Ketare

Yanzu yawan kayayyakin da kasar Sin ke fitarwa zuwa Amurka ya tsaya a kashi 15 cikin 100, inda ya ragu daga kashi 20 cikin 100 a shekarar 2018, lamarin da ke nuni da cewa, kasar Sin ba ta dogara ga Amurka kadai ba wajen yawan kayayyakin da take fitarwa zuwa kasashen waje ba. A sa’i daya kuma, kayayyakin kasar Sin ne kayayyaki mafi ingancin farashi kuma mafi yawa da Amurka ke shigowa da su, wanda ke amfanar mabukatada masana’antun Amurka. A hakikanin gaskiya, wannan yunkuri na samar da guraben ayyukan yi da dama a Amurka, yana nuna cudanya da moriyar juna na dangantakar cinikayya tsakanin Sin da Amurka. Girman cinikin ketare na kasar Sin ya nuna yadda ta ke kara mai da hankali kan fadada huldar da ke tsakaninta da kasashe masu tasowa da kuma kasashen da ke kawance da juna, ya kuma nuna cewa, kasar na rage dogaro ga kasuwannin yammacin duniya, musamman Amurka da Tarayyar Turai. Abu mafi mahimmanci shi ne ba za a iya dakile ci gaban kasar Sin a fannin fasaha ta hanyar shingen kasuwancin da ba shi da tushe balle marika ba. Kasar Sin za ta ci gaba da inganta kirkire-kirkire da karfafa matsayinta na kasancewa kan gaba a fannin cinikayya da fasaha a duniya, tare da karkata akalar kayayyakin da take fitarwa zuwa kasashen waje, ta hanyar mai da hankali kan kayayyakin fasahar zamani, da suka hada da motoci masu amfani da lantarki, da na’urorin dab’a na 3D, da na’urorin fasahar kere-kere, wadanda dukkansu ke samun ci gaba mai karfi, ta yadda za ta mayar da kasar daga masana’antar kera kayayyaki masu rahusa, zuwa kasa mafi girma a duniya a fannin fasaha da kirkire-kirkire. Haka ma sabbin nau’o’in cinikayya, irin su cinikayyar intanet tsakanin kasashe na kara habaka, wanda ya kara kaimi ga karfafa kasar Sin a kasuwannin duniya. Idan aka yi la’akari da ci gaban kariyar cinikayya, da takaddamar cinikayya ta hanyar kakaba haraji da kudin fito kan kayayyaki da kuma kalubalen yanayin siyasa, tabbas ana samun karin damuwa game da makomar dunkulewar duniya. Amma duk da haka matakan cinikayya maras shinge sun kasance ginshikan tattalin arzikin duniya mai fa’ida, saboda ciniki cikin ‘yanci yana habaka wadata, da samar da fa’ida ta zamantakewa da samar da karin ayyukan yi. La’akari da cewa, habaka masana’antu masu inganci da takara, da yin ciniki cikin ‘yanci suna baiwa kasashe damar samun bunkasa a duniya.

Ci gaba da kudurin kasar Sin na bude kofa ga kasashen waje da yin hadin gwiwa a fannin cinikayya da tattalin arziki, ya nuna matsayinta na babbar kasa mai karfin tabbatar da zaman lafiya a duniya, kana mai goyon bayan samun bunkasuwa tare. Don haka, ya kamata Amurka da EU su mai da hankali kan samar da ingantacciyar takara da kasar Sin maimakon daukar matakan kariyar cinikayya don dakile ci gaban kasar Sin, saboda hakan zai kawo cikas ga kirkire-kirkire da ci gaban tattalin arziki. Maimakon gina shingaye na kasuwanci da aiwatar da tsare-tsare masu hana ruwa gudu, kamata ya yi su zuba jari wajen gudanar da bincike da ci gaba, musamman a fannin fasahar kere-kere, don kara karfin takara a duniya. Hakazalika, ta hanyar ba da shawarar yin kasuwanci a bude, da kafa dabarun kasuwanci da hadin gwiwar zuba jari, da aiwatar da manufofin inganta sabbin abubuwa, Amurka da EU za su iya samar da damar tattalin arziki da za su amfanar da jama’arsu da kasuwancinsu. Bin tafarkin tsaftatacciyar takara, maimakon halin adawa, zai taimaka musu wajen habaka karfin tattalin arziki da samun jagoranci a duniya.

Bunkasar GDPn Manyan Biranen Sin Na Tasiri Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin

Bunkasar tattalin arziki Sin na da nasaba da bunkasar GDPn manyan birane 27 wanda ya zarce yuan tiriliyan 1 a shekarar 2024. Jimillar kayayyakin cikin gida na biranen kasar Sin 27 ya zarce yuan tiriliyan 1 kwatankwacin dalar Amurka biliyan 137.87 a shekarar 2024, kamar yadda jaridar People’s Daily a ketare ta bayyana a ranar Litinin 17 ga watan Fabrairun 2025. Alal misali, Shanghai, cibiyar hada-hadar kudi ta kasar Sin, da kuma birnin Beijing, babban birnin kasar, sun samu matsayi na daya da na biyu a kididdigar da aka yi, inda a shekarar 2024, adadin GDPnsu ya kai yuan tiriliyan 5.39 da yuan tiriliyan 4.98 bi da bi. Shenzhen, Chongqing da Guangzhou kowanne sun zarce yuan tiriliyan 3 a GDP, yayin da Suzhou, Chengdu, Hangzhou da Wuhan suka zarce yuan tiriliyan 2 a bara. Hakazalika, birane shida sun samu karuwar GDP sama da kashi 6 cikin dari, inda Quanzhou ke kan gaba da kashi 6.5 cikin dari. Wadannan birane gaba daya suna da ingantaccen tsarin masana’antu da manyan masana’antu. Masana’antu a wadannan biranen sun hada da masana’antar kere-kera da samarwa, da masana’antar ba da hidimomi na zamani da sabbin fasahohin kimiyya da fasaha, wadanda ke samar da tsarin kasuwanci iri-iri. Wadannan biranen suna mai da hankali kan habakar tattalin arzikin da ke haifar da kima, suna alfahari da karfin bincike na kimiyya, wanda ke ba da damar ci gaba da habaka masana’antu da sauyi. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
  • Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
  • Abubuwan Da Suka Ta Da Kura A Litttafin Janar Babangida
  • Habasha Da Somaliya Sun Cimma Yarjeniyoyin Fahimtar Juna A Tsakaninsu
  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Janye Bincike Kan Shigo Da Jan Karfe
  • Gwamnatin Jigawa Ta Biya  Sama Da Naira Miliyan 730 Ga Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya
  • Sheikh Na’im Kasim Ya Gana Da Ministan Harkokin wajen Kasar Iran Da Shugaban Majalisar Dokoki
  • An Nada Obasanjo Mai Shiga Tsakani A Rikicin Congo