Aminiya:
2025-03-31@04:22:54 GMT

Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗin 2025 na N54.99trn

Published: 1st, March 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sanya hannu kan kasafin kuɗin shekarar 2025 da ya kai Naira tiriliyan 54.99.

A ranar 13 ga watan Fabrairu, 2025, Majalisar Dokoki ta amince da kasafin bayan tattaunawa da nazari a kansa.

Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano Gwamnatin Sakkwato ta nemi malaman Jami’a su janye yajin aiki 

A baya dai, Shugaba Tinubu ya gabatar da kasafin da ya kai Naira tiriliyan 49.

7, amma daga bisani aka ƙara adadin kuɗin.

Shugaba Tinubu ya rattaba hannu kan kasafin a ranar Juma’a, a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Kasafin kuɗin na 2025 ya ninka wanda aka yi a bara, wanda ya tsaya a Naira tiriliyan 27.5, da ƙarin kashi 99.96 cikin 100.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo

’Yan Sanda sun kama mutum 14 da ake zargi da hannu a kisan matafiya 16 ’yan Arewa a kan titin Uromi zuwa Obajana, a Jihar Edo.

Sufeto-Janar na ’Yan Sanda (IGP), Kayode Egbetokun, ya yi tir da wannan hari, kuma ya bai wa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Hedikwatar Rundunar da ke Abuja, yin bincike.

Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja

Bayan faruwar lamarin, rundunar ’yan sandan Jihar Edo, ta tura jami’anta zuwa yankin domin wanzar da zaman lafiya.

Har ila yau, ana ci gaba da farautar sauran waɗanda suka tsere.

Kakakin rundunar ’yan sanda, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce Sufeto-Janar ya ba da umarnin a kamo waɗanda ke da hannu a lamarin.

Ya tabbatarwa da al’umma cewa ’yan sanda ba za su yarda da kisan gilla ba, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.

Sufeto-Janar ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu kuma su ba da haɗin kai wajen bincike.

Haka kuma, ya gargaɗi mutane kan ɗaukar doka a hannunsu, tare da tunatar da su cewa mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba laifi ne.

’Yan sanda sun kuma gargaɗi jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu, tare da kiran su da su riƙa kai rahoton duk wani abu da suka gani wanda ba su yarda da shi ga hukumomin tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari
  • Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo
  • Wike Ya Jinjina Wa Tinubu kan Bunkasa Ilimi Mai Zurfi
  • Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025
  • Manyan Amfanin Gona Biyar Da Ya Kyautu Manoma Su Zuba Hannun Jari A 2025
  • Tinubu Ya Ba Da Umarnin Kamo Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Kisan ’yan Arewa a Edo ya tayar da ƙura
  • GORON JUMA’A 28-03-2025
  • Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio
  • ’Yan sanda sun ƙwato wa mutumin da aka sace kuɗin fansarsa a Kano