Bayan da Mr. Donald Trump ya sake hawan kujerar shugaban kasar Amurka, ya dakatar da kusan dukkan gudummawar da kasarsa ke samarwa ga kasashen ketare, bisa manufarsa ta wai “Amurka ta zamanto gaba da komai”. Sai dai a kwanakin baya, gwamnatin kasar Philippines ta sanar da cewa, Amurka ba ta dakatar da gudummawar soja ta kimanin dala miliyan 336 a gare ta ba.

To, amma me Amurka take iya samu daga gudummawar soja da take samarwa Philippines har ya sa ba ta dakatar ba? Dalili shi ne gudummawar na iya sa sojoji da ‘yan sanda da ma ‘yan siyasa na kasar ta Phillipines su taimaka mata cimma manufarta, musamman ma wajen neman dakile kasar Sin bisa ga yadda suke sa-in-sa a batun tekun kudancin kasar Sin.

Sai dai kuma, a yayin da hakan ke biyan bukatun wasu ’yan siyasar Amurka, a sa’i daya kuma yana lalata moriyar kasar Phillipines.

Kasar Philippines na mai da kanta saniyar ware, musamman sabo da yadda sauran kasashen shiyyar ke neman tabbatar da zaman lafiya da ci gaba na yankin, kuma ita za ta dandana kudarta game da gudummawar soja da Amurka ta ba ta. Kuma sam hakan ba zai gurbata yanayin zaman lafiya na yankin tekun kudancin kasar Sin ba. (Lubabatu Lei)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Idan Shugaban Kasar Siriya Mai Ci Ya Taka Kasar Iraki Ana Iya Kama Shi

Shugaban kungiyar Asa’ib Ahl-Al-Hak, kungiya mai yaki da yan ta’adda a kasar Iraki, ya bayyana cewa idan shugaban kasar Siriya mai ci Abu Muhammad Al-Jolani ya kuskura ya taka kasar Iraki ana iya tsare shi sabuda gwamnatin kasar Iraki tana da sammashin kama shit un da dadewa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta nakalto shugaban kungiyar Qais Al-khazali yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Asabar, ya kuma kara da cewa jita jitan da yake ji na cewa shugaban kasar ta siriya zai zo iraki a nan gaba, bai taso ba, lokacin zuwansa kasar Iraki bai yi ba saboda zarge-zargen da ake masa tun kafin ya kwace shugabancin kasar ta Siriya, akwai matsalolin doka sosai wadanda za’a fuskanta.

Khazali ya kara da cewa, kyautata dangantaka tsakanin kasashen biyu bai da wata matsala, kuma yana amfanar kasashen biyu, amma zuwansa kasar Iraki a nan kusa yana da  matsala, don tun shekara 2014 Jolani shi ne babban kwamnadan HTS, kuma dakarunsa sun yaki dakarunsa a yaki da suka yi da yan ta’adda a lokacin.

Yace bangaren shari’a na kasar Iraki yana cin gashin kansa ne, bangaren zartarwa ba zai hana bangaren shara’a aikinsa ba.

Kafin haka dai firai ministan kasar Iraki Muhammad Shia al-sudani ya hadu da Jolqni a kasar Qatar a cikin yan kwanakin da suka gabata a gaban sarkin Qatar Tamim bin ahli thani

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gharibabadi : inganta sinadarin uranium jan layi ne a tattaunawar Iran da Amurka
  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Idan Shugaban Kasar Siriya Mai Ci Ya Taka Kasar Iraki Ana Iya Kama Shi
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar
  •  Abbas Arakci: Tattaunawa Da Amurka Ta Hanyar Shiga Tsakanin Oman Ta Shiga Sabon Zango
  • Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin
  • Iran Tace Yarjeniya Da Amurka Mai Yuwa Ne Idan Da Gaske Take
  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Hare Hare Kan HKI Da Jiragen Yakin Amurka
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya