Bayan da Mr. Donald Trump ya sake hawan kujerar shugaban kasar Amurka, ya dakatar da kusan dukkan gudummawar da kasarsa ke samarwa ga kasashen ketare, bisa manufarsa ta wai “Amurka ta zamanto gaba da komai”. Sai dai a kwanakin baya, gwamnatin kasar Philippines ta sanar da cewa, Amurka ba ta dakatar da gudummawar soja ta kimanin dala miliyan 336 a gare ta ba.

To, amma me Amurka take iya samu daga gudummawar soja da take samarwa Philippines har ya sa ba ta dakatar ba? Dalili shi ne gudummawar na iya sa sojoji da ‘yan sanda da ma ‘yan siyasa na kasar ta Phillipines su taimaka mata cimma manufarta, musamman ma wajen neman dakile kasar Sin bisa ga yadda suke sa-in-sa a batun tekun kudancin kasar Sin.

Sai dai kuma, a yayin da hakan ke biyan bukatun wasu ’yan siyasar Amurka, a sa’i daya kuma yana lalata moriyar kasar Phillipines.

Kasar Philippines na mai da kanta saniyar ware, musamman sabo da yadda sauran kasashen shiyyar ke neman tabbatar da zaman lafiya da ci gaba na yankin, kuma ita za ta dandana kudarta game da gudummawar soja da Amurka ta ba ta. Kuma sam hakan ba zai gurbata yanayin zaman lafiya na yankin tekun kudancin kasar Sin ba. (Lubabatu Lei)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya ce hare-haren da sojojin Amurka ke kaiwa kasar Yemen da keta hurumin yankunanta barazana ce karara ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa.

A cikin wata sanarwa da ya fitar yau Juma’a, Baghaei ya yi tir da hare-haren da Amurka ke kai wa Yemen ba bisa ka’ida ba, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula da raunata jama’ar kasar tare da lalata kayayyakin more rayuwa na kasar.

Ya ce ya kamata kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kawo karshen rashin daukar mataki da kuma yin shiru dangane da farmakin da sojojin Amurka ke kaiwa Yemen.

Ya ce Amurka na ci gaba da kai hare-haren soji kan kasar Yemen tare da kai hari kan kayayyakin more rayuwa na kasar domin daukar fansa kan hadin kan al’ummar Yemen da goyon bayan al’ummar Palastinu da ake zalunta.

Kakakin na Iran ya ce hare-haren na Amurka cin zarafi ne ga ka’idojin Yarjejeniya Ta Majalisar Dinkin Duniya da kuma ka’idojin dokokin kasa da kasa.

Baghaei ya dorawa gwamnatin Amurka alhakin aikata laifuka.

Kafofin yada labaran kasar Yemen sun ruwaito a safiyar yau Juma’a cewa, an kai wasu sabbin hare-hare a babban birnin kasar Yemen, inda aka kai hari kan wani sansanin soji a kudancin Sana’a da wasu hare-hare guda hudu.

An kuma kai hare-hare a yankunan da ke kusa da filin jirgin sama na Sana’a, baya ga gundumomi biyu a kudanci da tsakiyar lardin Sana’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Shugaba Xi Ya Jajantawa Shugaban Myanmar Game Da Girgizar Kasar Da Ta Auku
  • Siriya : Ofishin jakadancin Amurka ya yi gargadi game da yiyuwar hare-hare a yayin bikin sallah
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya
  • Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin
  • Iran Ta Bada Amsa Ga Wasikar Shugaban Kasar Amurka Ta Gayyatar Kasar Zuwa Tattaunawa Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Gwamnatin Amurka Tana Shirin Dakatar Da Bada Kudaden Tallafi Don Samar Da Wasu Magunguna