Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce za ta duba yiwuwar inganta cibiyar lafiya tare da kafa makarantar sakandare a garin Samamiya da ke karamar hukumar Birnin Kudu.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka a lokacin kaddamar da sabon masallacin Juma’a da gidan marayu da makarantar islamiyya, wanda dan asalin yankin Alhaji Muhammad Abubakar Samamiya ya gina a matsayin wakafi ga mahaifinsa.

Malam Umar Namadi ya bayyana jin dadinsa bisa wannan  kokari na Alhaji Muhammad Abubakar Samamiya.

Ya kuma bukaci masu hannu da shuni da su yi koyi da wannan matakin domin amfanin talakawa da marasa galihu a cikin al’umma.

Ya  jaddada aniyar gwamnatin jihar na ci gaba da yin aiki kafada da kafada da irin wadannan mutane a cikin al’umma.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, Gwamna Umar Namadi tare da rakiyar sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim, da ‘yan majalisar zartarwa na jiha, da shugaban karamar hukumar Birnin Kudu da sauran manyan baki  sun yi sallar Juma’a a sabon masallacin Abubakar Samamiya da ke karamar hukumar Birnin Kudu.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Ce Har Yanzu Akwai Guraben Biyan Kujerar Hajji

 

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna ta sanar da cewa har yanzu ana iya biyan kudin kujeran aikin Hajji ta hannun hukumar.

 

Jami’in Hulda da Jama’a na hukumar, Alhaji Yunusa Muhammad Abdullahi, ne ya bayyana hakan ta shafin sada zumunta na hukumar.

 

Ya yi kira ga wadanda har yanzu suke da bukatar zuwa Hajji su tuntubi jami’an hukumar a dukkan kananan hukumomi ashirin da uku na jihar ko su ziyarci hedikwatar hukumar dake kan titin Katsina, a cikin garin Kaduna.

 

Alhaji Yunusa Muhammad Abdullahi ya bayyana cewa mutum dubu uku da dari hudu da sittin (3,460) ne suka biya kudin Hajji ta hannun hukumar.

 

Ya kuma kara da cewa kudin Hajji ya kama naira miliyan takwas da dubu dari hudu da hamsin da bakwai da dari shida da tamanin da biyar, da Kobo hamsin da tara (₦8,457,685.59).

 

Rel/Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano
  • NAHCON Ta Naɗa Sabon Sakatare
  • GORON JUMA’A
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Ce Har Yanzu Akwai Guraben Biyan Kujerar Hajji
  • Boko Haram: An lalata gidaje da makarantu a ƙauyukan Adamawa
  • Sarkin Musulmi ya ba da umarnin dubin watan Ramadan
  • Gwamna Sule Ya Hori Masu Ziyarar Ibada Ta Kirista Su Zama Jakadu Na Gari
  • Gwamna Namadi Ya Nada Jami’an Alhazai 27 Tare Da Kara Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
  • Hamas ta yi tir da matakin Isra’ila na shirin takura masu ibada a masallacin Quds