Leadership News Hausa:
2025-04-21@06:57:37 GMT

SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

Published: 1st, March 2025 GMT

SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

1.1 Abinci sahur yana da albarka; yin sahur albarka ne, haka ma abincin sahur abinci ne mai albarka.

Ana karɓo hadisi daga Miƙdãm ɗan Ma’adikarib Allah ya ƙara yarda a gare shi, daga Annabi (S.A.W) ya ce: “Ina horonku da cin abincin sahur, domin abinci ne mai albarka” Nasã’i (Almujtabã 4/149 da Sunanul Kubrã 2/115) da Ahmad (Musnad #17192) da salsala ingantacciya.

An karɓo daga Abud Dardã’i Allah ya ƙara yarda a gare shi, ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Shi sahur abinci ne mai albarka.”Ibnu Hibban (Al’ihsãn #3464) Ɗabarãni (Mu’ujamul Kabir 17/131 hadisi mai lamba 322).

An karɓo daga Irbãdu ɗan Sãriyatu Allah ya ƙara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya gayyace ni cin abincin sahur a cikin Ramalana sai ya ce: ” Tawo ka ci abinci mai albarka” Abu Dãwud (#2344) da Nasã’i (Almujtabã 4/148) da Ibnu Hibbãn (Al’ihsãn #3465) salsalar hadisin ingantacciya ce. A lafazin Nasã’i ya zo da ce: Na ji Manzon Allah (S.A.W) Yana gayyatar mutane cin abincin sahur a cikin Ramalana…

1.3 Allah yana yabon masu yin sahur, Mala’iku kuma suna yi musu addu’a.

An barɓo hadisi daga Abdullahi ɗan Umar, Allah ya ƙara yarda a gare su, ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Lalle Allah yana yabon Mala’iku kuma suna addu’a ga waɗanda suke yin sahur” Ibnu Hibbãn (Al’ihsãn #3467) da Ɗabarani (Mu’ujamul Ausaɗ 6/287) da salsala ingantacciya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadan Allah ya ƙara yarda a gare mai albarka

এছাড়াও পড়ুন:

Bikin Easter : Paparoma Francis ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza

Shugaban mabiya darikar Katolika na duniya Fafaroma Francis, ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza.

A cikin sakonsa na bikin Easter, Paparoma ya yi tir da halin da ake ciki na jin kai a Gaza tare da yin kira da a tsagaita wuta.

Paparoma Francis ya halarci bukukuwan Ista a wannan Lahadi, inda ya yi tir da halin da ake ciki na jin kai mai daukan hankali a Gaza.

 “Ina kira ga bagarorin da su tsagaita wuta, a saki wadanda aka yi garkuwa da su, a kuma kai kayan agaji ga al’ummar falasdinu da kuma fatan samun zaman lafiya a nan gaba,” in ji shi a cikin sakonsa, wanda wani na hanun damansa ya karanto daga cocin St. Peter’s Basilica dake binrin Rome.

Jawabin nasa wani bangare ne na bikin Easter kamar yakke ake a ko wacce shekara, saidai fafaroman bai samu karanto jawabinba sabo lalurar ta rashin lafiya da yake fama da ita.

Mabiya addinin Kirisita a fadin duniya kan gudanar da bukukuwan Easter duk shekara domin tunawa da gicciyewa da kuma tashin Yesu Almasihu daga cikin matattu.

Bikin dai a kan fara shi ne tun daga dare irin na Alhamis zuwa wayewar garin Juma’a a kuma kammala a ranar Litinin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • Bikin Easter : Paparoma Francis ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza
  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan Almujtaba (a) 110
  • Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista
  • Minista Ya Sake Jaddada Ƙudirin Sabunta Kayan Aikin Watsa Labarai Na Gwamnati
  • GORON JUMA’A
  • Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.