HausaTv:
2025-04-21@11:51:41 GMT

Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka

Published: 1st, March 2025 GMT

Fira ministan hakar Habasha  Abiy Ahmed ya sami kyakkyawar tarba daga shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mamhud a birnin Mogadishu na Habasa a ranar Alhamis da ya kai ziyara domin bunkasa alaka a tsakainin kasashen biyu.

Sabani a tsakanin kasashen biyu masu makwabtaka da juna ya kunno kai ne a shekarar da ta gabata, bayan da kasar ta Habasha ya kulla yarjejeniya da yankin Somaliland akan tashar jirgin ruwa.

Ita dai kasar ta Habasha ba ta da iyaka da ruwa, don haka take son amfani da mashigar ruwan kasar ta yankin Somaliland. Habashan dai tana son gina wani yanki na kasuwanci a gabar ruwan  ta yankin Somaliland.

 Yankin Somaliland na kasar Somaliya ne wanda Mogadishu  take daukar cewa ba kasa ce mai cin gashin kanta.

Somaliya ta nuna fushinta akan waccan yarjejeniyar tare da zargin Habasha da yin kuste a cikin iyakokin kasarta.

A cikin watan Disamba ne dai Turkiya ta fara shiga tsakanin kasashen biyu domin  warware sabanin da yake a tsakaninsu.

Tattaunawar ranar Alhamis din a tsakanin kasashen biyu ta mayar da hankali ne akan kasuwanci, da tsaro da kuma batun sake mayar da alakar da diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja

An tabbatar da rasuwar mutum uku tare da asarar gonakin shinkafa da faɗinsu ya kai hekta dubu 10 a Jihar Neja a sakamakon mummunar ambaliyar ruwa.

Wannan ibtila’i ya faru ne a Ƙaramar Hukumar Mikawa, sakamakon sakin ruwa daga Madatsar Ruwa ta Jebba.

Shaidu sun bayyana cewa ambaliyar ta yi ɓarna sosai a gonakin yankin.

Shugaban Ƙungiyar Raya Yankin Kede, Abdulraham Abdulƙadir Kede-Wuya, ya ce gonar shinkafarsa mai faɗin hekta uku na daga cikin waɗanda suka salwanta a ambaliyar.

Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi

Ya ce, “gonata mai faɗin hekta uku na daga cikin waɗanda ruwan ambaliyar ya shanye, Sannan akwai sauran masu gonaki. Duk gonakin da bain ya shafa sun kai lokacin girbi. Ba mu san abin da ya da suka saki ruwan a irin wannan lokaci ba tare da sanar da al’umma ba.”

Wani manomi a yankin, Ibrahim Ndako, ya bayyana ambaliyar a matsayin bala’i, yana mai kira ga hukumomi su kawo musu ɗauki.

Ibrahim ya bayyana cewa, “Irin asarar asarar rayuka da maƙudan kuɗaɗe da wahalhalun da manoman rani suka tafka a sakamakon wannan abu, da wuya a iya mayar da shi.”

Ya ce yawancin manoma sun zo yankin ne daga jihohi Kebbi, Sakkwato, Zamfara Kano da Borno, domin yin noman rani a yankin, amma yanzu an jawo musu asarar.

Aminiya ta samu labarin cewa wasu daga cikin manoman sun fara girbi a lokacin da ambaliyar ta auku.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Daraktan Yaɗa Labarai na Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Ibrahim Aufu Hussaini ya ce an samu asarar rayukan ne a lokacin da wani kwalekwale ɗauke da su yake ƙoƙarin tsallake kogi da su bayan ambaliyar.

Ya bayyana cewa hukumar tana ci gaba da bincike domin tantance girman asarar da aka yi a sakamakon ambaliyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja
  • Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI
  •  Abbas Arakci: Tattaunawa Da Amurka Ta Hanyar Shiga Tsakanin Oman Ta Shiga Sabon Zango
  • Dakarun Gwagwarmayar Yemen Sun Kai Hare-Haren Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Mayakan Kungiyar Ta’addanci Ta ISIS Sun Sake Kunno Kai A Garuruwan Deir ez-Zor Da Hasaka Na Siriya
  • Iran da Amurka na shirin tattaunawa ta biyu a birnin Rome
  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki
  • Iran Tace Yarjeniya Da Amurka Mai Yuwa Ne Idan Da Gaske Take
  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya