HausaTv:
2025-03-31@14:46:09 GMT

Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka

Published: 1st, March 2025 GMT

Fira ministan hakar Habasha  Abiy Ahmed ya sami kyakkyawar tarba daga shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mamhud a birnin Mogadishu na Habasa a ranar Alhamis da ya kai ziyara domin bunkasa alaka a tsakainin kasashen biyu.

Sabani a tsakanin kasashen biyu masu makwabtaka da juna ya kunno kai ne a shekarar da ta gabata, bayan da kasar ta Habasha ya kulla yarjejeniya da yankin Somaliland akan tashar jirgin ruwa.

Ita dai kasar ta Habasha ba ta da iyaka da ruwa, don haka take son amfani da mashigar ruwan kasar ta yankin Somaliland. Habashan dai tana son gina wani yanki na kasuwanci a gabar ruwan  ta yankin Somaliland.

 Yankin Somaliland na kasar Somaliya ne wanda Mogadishu  take daukar cewa ba kasa ce mai cin gashin kanta.

Somaliya ta nuna fushinta akan waccan yarjejeniyar tare da zargin Habasha da yin kuste a cikin iyakokin kasarta.

A cikin watan Disamba ne dai Turkiya ta fara shiga tsakanin kasashen biyu domin  warware sabanin da yake a tsakaninsu.

Tattaunawar ranar Alhamis din a tsakanin kasashen biyu ta mayar da hankali ne akan kasuwanci, da tsaro da kuma batun sake mayar da alakar da diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Yakin Neman Zabe A Kasar Gabon

Jam’iyyun siyasa a kasar Gabon sun fara yakin neman zabe wanda za’a gudanar a ranar 12 ga watan Afrilu na wannan shekara ta 2025 a jiya Asabar.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto shugaban kasar Riko Brice Clotaire Oligui Nguema wanda ya jagoranci juyin mulki wa tsohon shugaban kasar Ali Bongo, sannan daga baya ya sauka don ya sake dawowa da hanyar zabensa ya fara yakin neman zabe a jiya, inda yake kira ga mutanen kasar su zabe shi saboda kyautatuwar kasar Gabon.

A cikin watan Augustan shekara ta 2023 ne sojoji suka kifar da gwamnatin Ali Bongo wanda ya gaji babansa Umar Bongo bayan rasuwarsa ba tare da zabe ba.

A halin yanzu dai yan takara 8 ne suke neman wannan kujerar a zaben ranar 12 ga watan Afrilu. Idan ba’a sami wanda ya lashe zaben ba za’a sake gudanar da zabe tsakanin wadanda suka zo na daya da kuma na biyu a zagayen farko.

Shugaban kasa a Gaban, yana yin shugabnci na tsawon shekaru 7 a zagaye na farko idan ya sake tsayawa ya kuma ci zabe yayi zagaye na 2 wanda zai kaishi ga shekari 14 na shugabaci. Daga nan shi ba zai tsaya ba, kuma wani daga cikin danginsa ba zai tsaya ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fara Yakin Neman Zabe A Kasar Gabon
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran
  • Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  •  Kasashen Iran Da Tunisya Suna Shirin Bunkasa Alaka A Fagagen Yawon Bude Ido
  • Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644
  • MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu
  • Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne