Leadership News Hausa:
2025-04-01@08:53:21 GMT

Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Kan Kiwon Kifi

Published: 1st, March 2025 GMT

Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Kan Kiwon Kifi

Bayanai Hudu Da Ya Kamata A Sani Dangane Da Kiwon Kifi A Nijeriya:

1- Kimanin Kashi 40 Kacal Ake Iya Cimma Bukatar Samar Da Shi A Nijeriya:

A cewar wata kididdiga ta Bankin Duniya, Nijeriya a 2018, ta samar da yawan Kifin da ya kai kimanin 1,169,478, wanda ya kai kimanin kashi 40 cikin 100, wanda bukatarsa da ake da ita a Nijeriya a shekara daya, ta kai kimanin tan miliyan 3.

4, inda sauran wanda ake bukatar fitarwa waje ya kai kashi 60 cikin 100.

2- Kamun Tarwada A Nijeriya Fitacciyar Sana’a Ce:

Samar da Tarwada a Nijeriya, ya karu daga tan miliyan 21,700 a 1999 zuwa tan miliyan 316,700 a 2015, wanda ya karu da sama da kashi 1,400 a cikin shekaru 25 da suka wuce.

Shugaban kungiyar masu kamun Tarwada na kasa (CAFAN), Cif Tayo Akingbolagun a cikin sanarwar da ya fitar a taron shekara na kungiyar ya bayyana cewa, Nijeriya a 2016 ta samar da sama da tan 370,000 na Tarwada.

3- Nijeriya Ce Ta Uku Kan Gaba A Afirka Wajen Kamun Kifi:

Wani rahoto na 2018 da Bankin Duniya ya fitar ya nuna cewa, jimillar Kifin da aka samar a duniya ya nuna cewa, a yanzu Nijeriya ce ta uku da ke kan gaba a Afirka wajen samar da Kifi, inda ta samar da kimanin tan 1,169,478.

4- Kiwon Kifi Na Bunkasa Tattalin Arzikin Nijeriya Da Kashi 3.24:

A cewar wasu bayanai da Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar a zango na daya na 2021, fannin Kiwon Kifi ya bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin Nijeriya da kimanin kashi 3.24.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka kan kashe ’yan Arewa a Edo — Sarkin Musulmi

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya bayyana rashin jin daɗinsa dangane da kashe matafiya ’yan Arewa da aka yi a Jihar Edo.

Saboda haka Sarkin ya ce suna dakon ganin hukuncin da za a ɗauka dangane da faruwar wannan mummunan lamari.

Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka Dalilin da muka soke Hawan Bariki — Masarautar Zazzau

Da yake miƙa saƙon gaisuwar Sallah ga Gwamnan Sakkwato, Alhaji Ahmad Aliyu a ranar Litinin, Sarkin ya ce “mun ga an ɗauki mataki kan yanayin da ake ciki a Jihar Edo.

“Saboda haka muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka bayan kammala bincike don ba wani dalili ka kashe mutum ba tare da wani haƙƙi ba.

“Muna kiran jami’an tsaro da su tashi tsaye domin tabbatar da cewa jama’a ba su fusata ba sun ɗauki hukunci a hannunsu.

“Idan a wani wurin mutanen banza sun ɗauki hukunci a hannunsu, mu a nan Sakkwato ba za mu bari a yi abin da bai kamata ba.

“Mu sanya ’yan uwanmu da abin ya faru da su a cikin addu’a sannan muna kiran gwamnati da jami’an tsaro su ɗauki matakin kare rayukkan jama’a,” a cewar Sarkin Musulmi.

Sarkin ya ƙara da cewa “bai kamata a riƙa yaɗa abin da bai dace ba a kafafen sadarwa na zamani da za su janyo tashin hankali a wurin da ake da zaman lafiya.

“Duk wani abu da ya faru a wani wuri, bai kamata wasu da ke can wani wurin na daban su ce za su ɗauki mataki a Sakkwato ko Kano ko Kaduna kan wani abun da ya faru a Jihar Edo ko Legas ba.”

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Za Su Kwaɗaita Muku Azumtar Sitta Shawwal
  • Muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka kan kashe ’yan Arewa a Edo — Sarkin Musulmi
  • Sani Ahmad Lere Na Radio Nijeriya Kaduna Ya Zama Falakin Lere
  • Gwamnati Za Ta Inganta Wuraren Tarihi Domin Nishadantarwa A Duk Jihohin Nijeriya 
  • Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
  • Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Legas, Mutane 10 Sun Kamu
  • Abubuwan da ya kamata Musulmi ya yi a ranar Karamar Sallah
  • Gobe take Sallah a Nijeriya
  • Gobe take Sallah a Nijeriya — Sarkin Musulmi
  • Abubuwan da Za ki Runguma domin Burge Mijinki