Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Kan Kiwon Kifi
Published: 1st, March 2025 GMT
Bayanai Hudu Da Ya Kamata A Sani Dangane Da Kiwon Kifi A Nijeriya:
1- Kimanin Kashi 40 Kacal Ake Iya Cimma Bukatar Samar Da Shi A Nijeriya:
A cewar wata kididdiga ta Bankin Duniya, Nijeriya a 2018, ta samar da yawan Kifin da ya kai kimanin 1,169,478, wanda ya kai kimanin kashi 40 cikin 100, wanda bukatarsa da ake da ita a Nijeriya a shekara daya, ta kai kimanin tan miliyan 3.
2- Kamun Tarwada A Nijeriya Fitacciyar Sana’a Ce:
Samar da Tarwada a Nijeriya, ya karu daga tan miliyan 21,700 a 1999 zuwa tan miliyan 316,700 a 2015, wanda ya karu da sama da kashi 1,400 a cikin shekaru 25 da suka wuce.
Shugaban kungiyar masu kamun Tarwada na kasa (CAFAN), Cif Tayo Akingbolagun a cikin sanarwar da ya fitar a taron shekara na kungiyar ya bayyana cewa, Nijeriya a 2016 ta samar da sama da tan 370,000 na Tarwada.
3- Nijeriya Ce Ta Uku Kan Gaba A Afirka Wajen Kamun Kifi:
Wani rahoto na 2018 da Bankin Duniya ya fitar ya nuna cewa, jimillar Kifin da aka samar a duniya ya nuna cewa, a yanzu Nijeriya ce ta uku da ke kan gaba a Afirka wajen samar da Kifi, inda ta samar da kimanin tan 1,169,478.
4- Kiwon Kifi Na Bunkasa Tattalin Arzikin Nijeriya Da Kashi 3.24:
A cewar wasu bayanai da Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar a zango na daya na 2021, fannin Kiwon Kifi ya bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin Nijeriya da kimanin kashi 3.24.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90% a jihar
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya sanar da rage kashi 90% na tallafin rabon kayan abinci don ƙarfafa dogaro da kai a tsakanin mazauna jihar.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da yake ƙaddamar da rabon kayan abinci ga magidanta 25,000 gabanin watan Ramadan a Maiduguri, Jere da sauran sassan jihar.
Helikwaftan farko ƙirar Najeriya zai fara aiki —NASENI Sarkin Musulmi ya ba da umarnin dubin watan RamadanA cewar Zulum, gwamnatin jihar za ta ba da fifiko ga hanyoyin samar da ci gaba na tsawan lokaci a kan matakan agaji na gajeren lokaci kamar rabon tallafin abinci.
Ya kuma bayyana irin gagarumin jarin da gwamnatinsa ta yi wajen tallafa wa manoma sama da miliyan ɗaya da muhimman kayayyakin amfanin gona kamar irin su iri, taki, famfunan ban-ruwa, maganin ƙwari da magungunan kashe ciyawa.
“Wannan dabarar ba kawai za ta inganta dogaro da kai ba ce har ma da rage kashe kuɗaɗen gwamnati,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, rabon kayan tallafin zai taƙaita ne ga ƙananan hukumomin jihar guda biyu kawai daga cikin 27 a shekarar 2025 saboda ƙalubalen da suke fuskanta.
“Ƙananan Hukumomin da za su sami tallafin abinci a shekara mai zuwa su ne: Ngala da Kala-Balge saboda yanayi na musamman.
“Waɗannan yankuna sun fuskanci mummunar ɓarna a gonakinsu daga giwaye kuma sun fuskanci ambaliyar ruwa. Don haka, a shekarar 2025, gwamnatin Jihar Borno za ta samar da kayayyakin tallafin abinci ga Ngala da Kala-Balge kaɗai,” inji shi.