Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
Published: 1st, March 2025 GMT
Tsohon Shugaban Hukumar Kula da Matasa Masu Yi Wa Ƙasa Hidima (NYSC), Manjo Janar Maharazu Tsiga (mai ritaya), ya kuɓuta bayan shafe kwana 22 a hannun ’yan bindiga.
An sace shi ne a ranar 6 ga watan Fabrairu, 2025, a gidansa da ke garin Tsiga a Ƙaramar Hukumar Bakori a Jihar Katsina, yayin da wasu ’yan bindiga suka kai hari.
Maharan sun nemi kuɗin fansa Naira miliyan 250 kafin su sako shi.
Sai dai bayan tattaunawa, an biya kuɗin fansa, wanda ya kai ga sakinsa.
A halin yanzu, likitoci na kula da shi a wani asibiti da ba a bayyana ba sunansa ba.
A lokacin kai harin, sama da ’yan bindiga 100 ne suka afka gidansa, suka yi awon gaba da shi da wasu mazauna yankin.
Wasu mutum biyu sun samu raunuka yayin harin, yayin da wani daga cikin ’yan bindigar ya harbi ɗan uwansa bisa kuskure, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa.
Har yanzu, rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ba ta fitar da wata sanarwa kan sakin tsohon shugaban NYSC ɗin ba.
Satar mutane da hare-haren ‘yan bindiga na ci gaba da zama babbar barazana ga tsaro a Jihar Katsina da sauran sassan Najeriya.
Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro na fuskantar matsin lamba wajen shawo kan wannan matsala.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Janar Tsiga mahara yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun ceto ɗalibai 10 sun lashe ɗan bindiga a Edo
Jami’an rundunar ’yan sandan jihar Edo sun ceto ɗalibai 10 da wasu ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Edo.
An kashe ɗaya daga cikin ’yan bindigan, a yayin musayar wuta da ’yan sanda a lokacin aikin ceto, yayin da sauran suka tsere da raunukan harbi.
Daily Trust ta ruwaito cewa an yi garkuwa da ɗaliban ne a ranar 16 ga Afrilu, 2025, a kan hanyarsu ta zuwa Jami’ar Babcock don taron shekara-shekara na GYC Africa.
Kakakin rundunar, SP Kontongs Bello, wanda ya tabbatar da ceton, ya ce da samu rahoton sace daliban, kwamishinan ’yan sandan jihar, Funsho Adegboye, ya tura ’yan sanda na musamman tare da ’yan banga da maharba cikin daji domin ceto su da kuma kama waɗanda ake zargi.
Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayiYa ce a lokacin aikin, an kashe ɗaya daga cikin ’yan garkuwan, yayin da sauran suka tsere da raunukan harsashi.
“Jami’an sun yi taka-tsan-tsan don guje wa asarar rayukan fararen hula saboda ’yan garkuwan sun yi amfani da waɗanda aka sace a matsayin garkuwa.”
A cewarsa, wani Sufeton ɗan sanda ya samu raunin harbin bindiga a lokacin aikin, kuma yana samun kulawa a asibiti a halin yanzu.
Ya ce ana ci gaba da ƙoƙarin cafke ‘yan garkuwan da suka tsere.