Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno
Published: 1st, March 2025 GMT
Wata gobara da ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Mandalari da ke Konduga a Jihar Borno, ta hallaka mutane biyu tare da jikkata wasu da dama.
Gobarar, ta tashi da misalin ƙarfe 11:25 na safiyar Juma’a, 28 ga watan Fabrairu, 2025, ta bazu zuwa yankunan da ke da cunkoson jama’a, inda ta cinye matsugunan wucin gadi da kuma kayayyaki masu tarin yawa.
Sojojin da aka jibge a Konduga, sun kai ɗauki nan take bayan samun labarin tashin wutar.
Sun haɗa kai da jami’an agaji da kuma al’ummar yankin domin shawo kan gobarar.
Duk da haka, akwai fargabar cewa yawan mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa.
Dakarun Operation Haɗin Kai da ke aiki a Konduga sun taka rawar gani wajen ceto mutane da kuma hana gobarar bazuwa.
“Sojoji sun kawo ɗauki cikin gaggawa, tare da tattara ma’aikata da kayan aiki don shawo kan gobarar da kare mutanen da lamarin ya shafa,” in ji wata majiya daga jami’an tsaro.
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Borno, tare da haɗin gwiwar sojoji da hukumomin agaji, na ci gaba da ƙoƙarin shawo kan lamarin.
Hakazalika, an tura ƙungiyoyin lafiya domin kula da waɗanda suka jikkata.
Wannan ba shi ne karon farko da sansanin Mandalari ke fuskantar irin wannan iftila’i ba.
Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, tsakanin watan Fabrairu da Yunin shekarar 2024, gobara ta tashi aƙalla sau 43 a sansanin, lamarin da ya haddasa asarar rayuka da dukiyoyi masu tarin yawa.
Shugaban al’ummar yankin, Bulama, ya yaba da ƙoƙarin jami’an tsaro a Konduga, inda ya ce suna bayar da muhimmiyar gudunmawa ba kawai wajen magance rikice-rikice ba, har ma da tabbatar da tsaron ’yan gudun hijira.
“Muna godiya ga taimakon Allah SWT da nasu, domin ba don agajin sojoji ba, da lamarin zai iya yin muni matuƙa,” in ji shi.
A halin yanzu, hukumomi sun buƙaci ’yan gudun hijira da su ƙara yin taka-tsantsan domin hana sake faruwar irin wannan gobara, musamman a wannan lokaci na zafi.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), na ci gaba da rabon kayan tallafi, yayin da hukumomin tsaro suka tabbatar da cewa za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara Sansanin yan gudun hijira yan gudun hijira
এছাড়াও পড়ুন:
An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
Mai martaba Sarkin zazzau,kuma shugaban majalisar sarakunan jihar kaduna, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya bukaci Dagatan da ke masarautar zazzau da su rinka sanya ido sosai akan zirga-zirgar bakin fuskokin da ba su gane ba a cikin su.
Ya yi kiran ne a sakon sa na sallah bayan kammala azumin watan Ramadan a fadar sa dake Zaria.
Ahmed Nuhu Bamalli ya bayyana cewa harkar tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a hakki ne na kowa amma ba gwamnati ita kadai ba,a don haka akwai bukatar ganin an hada karfi da karfe domin samun nasara a game da tsaron.
Mai martaba Sarkin ya kuma bukaci Dagatan da su rinka kai rahoton zuwan duk wani bako ko bakuwa da kuma dalilin zuwan.
Ya ce idan har aka dauki wannan matakin matsalar tsaro za ta ragu sosai,yana mai nuni da cewa sarakunan gargajiya na da muhimman rawar da za su taka game da tsaro.
Haka kuma Sarkin na zazzau ya bukaci iyaye da su rinka sanya ido game da harkokin yau da kullum na ‘ya’yan su.
Haka kuma ya gode wa gwamnan jihar kaduna da shugaban majalisar wakilai,Dr Abbas Tajuddeen, Iyan zazzau saboda irin aiyukan ci gaban da suke samar wa talakawa a zaria da sauran kananan hukumomin jihar kaduna.
A wani labarin kuma,Limamin masallacin juma’a na rukunin kananan gidajen dake kofar Gayan,Zaria, Sheikh Dalhatu Bello Amaru ya yi Allah wadai da kisar Gilla da wasu yan ta’adda suka yi wa wasu mafarauta yan arewa su 11 a Uromi da ke jihar Edo.
Ya yi Allah wadan ne a hudubar sa ta sallar idin karamar sallah da ya gudanar.
Ya ce mutanen Arewa ba su amince da kisar gillar da aka yi wa maharban ba gaira ba dalili.
Sheikh Bello Amaru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihar Edo da su tabbatar da ganin an kamo duk mutanen da suka aikata laifin domin suma a kashe su domin ran su bai fi na mafarautar da suka kashe ba tare da wani dalili ba.
Ya yi Bayanin cewa Allah ya bada umurnin cewa duk wanda ya kashe wani shima a kashe shi,amma hakan bai bada damar wani ya dsuki doka a hannun shi ba,hakki ne na hukumomin da abin ya shafa.
Haliru Hamza