Tawagar yan wasan Damben Gargariya ta kasar Iran sun zama zakara a wasan damben da ya gudana a birnin Tirana babban birnin kasar Albaniya a makon da ya gabata, inda suka tashi da lambobin yabo 6 wadanda suka hada da zinari 4 azurfa da tagulla.

Wannan nasara da ta maida kasar a matsayin zakara a wannan wata a fagen kasa da kasa.

Tawagar damben gargaji ta kasar Iran ita ce zakara a gasar damben na wannan shekara ta 2025 haka ita ce zakara a gasar shekara ta 2024.

An gudanar da gasar ne a ranakun 27-28 na watan Fabrayrun wannan shekara, wato 2025UWW, wanda ya jawo hankalin masu shaawar wasan a duniya.

Daga cikin yan wasan da suka sami lambar zinari sun hada har da  Ali Momini mai nauyin (57) Rahman Amouzad (65) Kamran Ghasempour da kuma Amir Hussain Zare.(125).

Sai kuma mai lambar  Azurfa, wato Erfan Alizadeh (97). Younes Emami (74kg) ya sami tagulla. Iran ta sami maki  97 sai kuma kasar Japan wacce ta zo na biyu da maki 93.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Yakin Neman Zabe A Kasar Gabon

Jam’iyyun siyasa a kasar Gabon sun fara yakin neman zabe wanda za’a gudanar a ranar 12 ga watan Afrilu na wannan shekara ta 2025 a jiya Asabar.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto shugaban kasar Riko Brice Clotaire Oligui Nguema wanda ya jagoranci juyin mulki wa tsohon shugaban kasar Ali Bongo, sannan daga baya ya sauka don ya sake dawowa da hanyar zabensa ya fara yakin neman zabe a jiya, inda yake kira ga mutanen kasar su zabe shi saboda kyautatuwar kasar Gabon.

A cikin watan Augustan shekara ta 2023 ne sojoji suka kifar da gwamnatin Ali Bongo wanda ya gaji babansa Umar Bongo bayan rasuwarsa ba tare da zabe ba.

A halin yanzu dai yan takara 8 ne suke neman wannan kujerar a zaben ranar 12 ga watan Afrilu. Idan ba’a sami wanda ya lashe zaben ba za’a sake gudanar da zabe tsakanin wadanda suka zo na daya da kuma na biyu a zagayen farko.

Shugaban kasa a Gaban, yana yin shugabnci na tsawon shekaru 7 a zagaye na farko idan ya sake tsayawa ya kuma ci zabe yayi zagaye na 2 wanda zai kaishi ga shekari 14 na shugabaci. Daga nan shi ba zai tsaya ba, kuma wani daga cikin danginsa ba zai tsaya ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi
  • An Fara Yakin Neman Zabe A Kasar Gabon
  • Iran Ta Zama Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Bakin Teku Karo Na 4 Asiya
  • Gwarzon gasar Alƙur’ani ya Kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina
  • Hezbulla: Iran Ce Babbar Mai Goyon Bayan Al-Ummar Falasdinu
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644
  • Wadanda Iftila’in Tankar Mai Ya Sha A Jigawa Sun Sami Naira Miliyan 4 Kowannensu
  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?
  • Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025