Aminiya:
2025-03-01@14:05:30 GMT

Gobara ta ƙone sashen wani asibiti a Legas

Published: 1st, March 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi cikin ta lalata wani ɓangare na Asibitin Ago da ke kan titin Ago Palace, Okota, a Jihar Legas.

Gobarar ta fara ne da misalin ƙarfe 8:30 na daren ranar Juma’a, inda ta shafi wani sashe na ginin mai bene hawa ɗaya, inda asibitin yake.

Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250

Likitoci da marasa lafiya da ke cikin asibitin sun tsere domin tsira da rayukansu yayin da wutar ta bazu.

Babban Sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Lagos (LASEMA), Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce jami’ansu sun isa wajen gobarar da misalin ƙarfe 8:45 na dare.

Binciken da LASEMA ta gudanar ya nuna cewa gobarar ta faru ne sakamakon matsalar wutar lantarki.

Rahotanni sun nuna cewar babu wanda ya rasa ransa ko ya jikkata.

Jami’an kashe gobara daga LASEMA da LRU da sauran masu bayar da agajin gaggawa sun haɗa kai don shawo kan gobarar tare da hana ta bazuwa zuwa wasu gine-gine da ke kusa da asibitin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta yanke wa matashi ɗaurin wata 6 kan satar kaza

Wata kotun majistare da ke zamanta a Ago Iwoye, Jihar Ogun, ta yanke wa wani matashi ɗan shekara 21, Adebanjo Segun, hukuncin ɗaurin watanni shida a gidan yari bisa samunsa da laifin satar kaza.

Jami’in hulɗa da jama’a na Hukumar tsaro ta Civil Defence , Dyke Ogbonnaya ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

An ce an fara samun matsalar ne a ranar Laraba, 19 ga Fabrairu, 2025, kan Adebanjo mai shekara 21 a lokacin da aka kama shi da laifin satar kaza.

Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno An shiga ruɗani bayan Obasa ya koma majalisar Legas da ’yan sanda

Ogbonnaya ya bayyana cewa, “Bayan an yi nazari sosai kan lamarin tare da kammala bincike, an gano cewa wanda ake tuhuma ya aikata irin wannan laifin a wani lokaci a watan Disambar 2024 inda aka yi masa afuwa a matsayin wanda ake zato da ya yi laifin farko.

“Saboda bayyana laifin da ya aikata a baya, an gurfanar da shi a gaban Kotun Majistare ta Ago-Iwoye kan tuhume-tuhumen da ya shafi sashe na 430 na dokokin manyan laifuka na Jihar Ogun, Nijeriya 2006, a ranar 20 ga Fabrairu, 2025.

“Bayan ya amsa laifinsa a gaban Alƙali ​​O.F. Adeduntan, an same shi da laifin kuma  kotun ta yanke masa hukuncin ɗaurin watanni shida a gidan yari.”

Hakazalika, an kuma yanke wa wani Kazeem Tobi mai shekara 20 hukuncin ɗaurin watanni shida a gidan yari bisa samunsa da laifin satar janareta na Elepaƙ wanda kuɗinsa ya kai kusan N120,000 kacal.

An ce an sake gurfanar da Tobi a ranar Talata, 4 ga watan Fabrairu, 2025, kuma bayan da aka yi nazari sosai a kan lamarin, an gurfanar da shi a gaban Kotun Majistare ta Ago-Iwoye kan tuhume-tuhume biyu da suka shafi haɗa baki wajen aikata laifi da kuma mallakar wani abu da ake zargin an sace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno
  • Noman Dabino: Jigawa Ta Yi Hadaka Da Saudiyya
  • Babu Wani Dan Arewa Mai Hankali Da Zai Yi Wa APC Kamfen A 2027 – PDP
  • Iran Za Ta Rubanya Samar Da Wutar Lantarki Ta Makamashin Nukiliya Har Sau Uku Zuwa 2029
  • Kotu ta yanke wa matashi ɗaurin wata 6 kan satar kaza
  • Boko Haram ta ƙona wuraren ibada da gidaje a Adamawa
  • Trump Ya Kawo Karshen Shirin Bunkasa Samar Da Wutar Lantarki A Afirka
  • Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N825 a Legas
  • Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas