Aminiya:
2025-04-01@03:04:12 GMT

Gobara ta ƙone sashen wani asibiti a Legas

Published: 1st, March 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi cikin ta lalata wani ɓangare na Asibitin Ago da ke kan titin Ago Palace, Okota, a Jihar Legas.

Gobarar ta fara ne da misalin ƙarfe 8:30 na daren ranar Juma’a, inda ta shafi wani sashe na ginin mai bene hawa ɗaya, inda asibitin yake.

Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250

Likitoci da marasa lafiya da ke cikin asibitin sun tsere domin tsira da rayukansu yayin da wutar ta bazu.

Babban Sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Lagos (LASEMA), Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce jami’ansu sun isa wajen gobarar da misalin ƙarfe 8:45 na dare.

Binciken da LASEMA ta gudanar ya nuna cewa gobarar ta faru ne sakamakon matsalar wutar lantarki.

Rahotanni sun nuna cewar babu wanda ya rasa ransa ko ya jikkata.

Jami’an kashe gobara daga LASEMA da LRU da sauran masu bayar da agajin gaggawa sun haɗa kai don shawo kan gobarar tare da hana ta bazuwa zuwa wasu gine-gine da ke kusa da asibitin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari

Tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa yana jin daɗin yadda shugaban ƙasar Bola Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa.

Buhari ya ce har yanzu Tinubu bai sauya ba daga tsari da manufofin da jam’iyyar APC ta kafa wanda har ya sanya shi kansa ’yan Nijeriya suka zaɓe shi a 2015.

An ga watan Sallah a Saudiyya Dalilin da Aminu Bayero ba zai iya jagorantar hawan Sallah ba — Kurawa

Buhari ya bayyana hakan a saƙonsa na taya Tinubu murnar zagayowar ranar haihuwarsa, wanda ya cika shekaru 73 a doron ƙasa.

Sanarwar da mai magana da yawun Buhari, Mallam Garba Shehu ya fitar a ranar Asabar, ta ce tsohon shugaban yana alfahari da alaƙarsa da shugaban ƙasar na yanzu.

Sanarwar ta ce Buhari da Tinubu sun gana ta wayar tarho a ranar Juma’a, inda a ciki Buhari ya yi Tinubu addu’ar tsawon rai da ingantacciyar lafiya da, sannan ya yi masa fatan samun nasarar a mulkinsa.

“Idan muka yi wa shugabanninmu addu’a, muna yi wa kanmu ne. Ƙasarmu na buƙatar addu’o’inmu,” in ji Buhari a ganawarsa da Tinubu.

Buhari ya ce shi da iyalansa suna godiya ga Tinubu da sauran jagororin jam’iyyar bisa ƙoƙarin da suka yi wajen kafa jam’iyyar APC, inda har ya samu nasarar zama shugaban ƙasa har sau biyu, bayan ya sha gwadawa a baya ba tare da samun nasara ba.

“Lokacin da ’yan Nijeriya suka zaɓi APC a 2023, zaɓi suka yi domin kafa tubalin sabuwar Nijeriya inda talakawa za su samu damarmakin da suke buƙata, kuma ina jin daɗi har yanzu ba a kauce daga tsarin ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Nanata Adawa Da Matakan Tilastawa Da Nuna Babakeren Tattalin Arziki
  • Muna so a nuna wa duniya mutanen da suka kashe ’yan Arewa a Edo — Gwamnan Kano
  • A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi
  • Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • Farashin fetur ya ƙaru sakamakon hana Dangote mai a Naira
  • Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Legas, Mutane 10 Sun Kamu
  • Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari
  • Najeriya : An samu hargitsi a yayin jerin gwanon ranar Kudus a Abuja
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon