A yau daya ga watan Maris ne dokar haramta amfani da tankunan dakon man fetur masu daukar lita 60,000 saboda yawan hatsarin da suke yi, wanda kuma yake lakume rayukan daruruwan mutane a ko wace shekara a duk fadin kasar.

Jaridar Weeken Trust ya bayyana cewa hukumar ‘ The Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA)’ ta haramta amfani da iran wadannan tankunan man ne daga yau Asabar 1 ga watan Maris, saboda ceton rayukan mutanen kasar.

Dokar dai zata shafi ayyukan mutanen, don wasu zasu rasa ayyukansu.

Dokar ta kara da cewa, daga yau tankunan man masu daukar lita 45,000 zuwa kasa ne kawai za’a a barisu dauki man fetur zuwa wasu wurar daga deport.

Sai kuma kungiyar masu dakon man fetur a kasar sun bayyana cewa zasu yi asarar tankuna na kimani   naira biliyon 300 saboda wannan haramcin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Diblomasiyyar Kasashen Rasha Da Amurka Zasu Sake Haduwa A Birnin Istambul A Gobe

Jami’an diblomasiyyar kasashen Rasha da Amurka zasu sake haduwa a gobe Alhamis 27 ga watan Fabarayru a birnin Istambul na kasar Turkiyya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov yana fadar haka a kasar Qatar, ya kuma kara da cewa a haduwarsu na gobe kasashen biyu zasu maida hankali ne wajen sake bude ofisoshin jakadancin kasashen biyu a kasashensu.

Ministan ya kara da cewa, dangantaka tsakanin Rasha da Amurka bai taba yin kyau ba tun lokacin tarayyar Soviet, amma ta dan kyautata a lokacin shugabancin Trump na farko.  Sannan bayan sake dawowan Trump da alamun dangantakar zata yi kyau.

A gobe Alhamis dai bangarorin biyu zasu dubu abubuwan da suke hana ruwa guda a ofisoshin jakadancin kasashen biyu a Washington da Mosco.

A ranar 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025 ne a karon farko tun bayan fara yakin Ukraine jami’an diblomasiyyar kasashen biyu suka hadu a birnin Riyad na kasar Saudiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Haleyen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (1)
  • Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
  • Yadda Matasa Ke Kara Shiga Harkar Tsaface-tsaface
  • Gwamna Sule Ya Hori Masu Ziyarar Ibada Ta Kirista Su Zama Jakadu Na Gari
  • Ɗangote Ya Rage Farashin Man Fetur Saboda Gabatowar Azumi
  • Jami’an Diblomasiyyar Kasashen Rasha Da Amurka Zasu Sake Haduwa A Birnin Istambul A Gobe
  • Mugunta Fitsarin Fako…
  • Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N825 a Legas
  • Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas