Haleyen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (1)
Published: 1st, March 2025 GMT
Dabi’un Da Suke Sa Malamin Makaranta Ya Ke Zama Nagartacce
Ko dai su kasance suna koyar da manyan dalibai ne ko kuma lamarin ya zama suna koyar da kirga ce daga daya zuwa goma Azakakuran Malamai suna da wadansu dabi’u da suka yi kama da juna. Alal misali sanin kowa ne duk dai masu ilimi ko masu harkar koyarwa suna da wata baiwa da tsayawa su saurarar maganar da ake fada/abin kuma ba ya tsaya kan lamarin dalibansu kadai ba,har ma abokan aikinsu, masu makarantu,da kuma iyayen daliban.
Kamar yadda bayanan Robert Lee, Ed.D., Shugaban Kwalejin ilimi ta Sanford dangane da hakan cewa yayi, “Abin so ne ace yana dabi’u da suka hada da babban abinda aka fi so shi ne ya kasance yana nau’oin basiru na iya mu’amala kwarai da gaske, tausayi, da kuma kauna da sha’awar aikin na koyarwa. Irin wadannan dabi’un ba kawai sun tsaya bane kan samar da hanyoyin / dabarun koyarwa masu kyau ba, akwai saw a dalibai son sun maida hankali kan abinda ake koya masu har ma akwai kai su ga hanyar samun nasarar karatu.Malamai wadanda suka san abinda suke yi suna da dabara ko halayya ta ta gane/ sanin darasin da suke koyarwa bugu da kari kuma sun san yadda za su koyawa dalibansu darasin ta hakan ne kuma zai zama masu abin alkhairi gare su. Ya kamata Malamai su rika karawa dalibansu kwarin gwiwa har sai ga sun kai iyakar mizanin da suke son zuwa ko kuma burinsu na karatu/,inda za a lura da kowane dalibi ana yi ma sa kallon yana da kima ta bangaren karatu/ilimin da suke bukata, suna girmmama kowa, yayin da su kuma ana ganin mutuncinsu/ girmansu.”
Duk da haka dai wasu dabi’un da ake bukata daga Malaman makaranta wasu ba su kai darajar wasu ba idan aka kalli amfanin da za a iya samu, wasu kuma da akwai matukar wuya idan ana son aiwatar da su, dukkan su dai suna da amfani ga Malamai ya zama sun sansu suna kuma aiwatar da su a harkar su ta koyarwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
A shekarar 2017, aka dauki matakin fadada kasashen da za su halarci gasar 2026 zuwa 48 bayan duka mambobin Fita sun kada kuri’ar amincewa da matakin, sannan a ranar 15 ga watan Mayu mai zuwa ne za a gudanar da taron FIFA na 75, kuma a nan ne za a tattauna bukatar ta Conmebol. Idan har aka amince da bukatar, gasar ta 2030 za ta kunshi karawa 128, daga karawa 64 da ake yi tsakanin 1998 zuwa 2022.
Masu sukar matakin dai na cewa fadada gasar zai rage darajar tsarin da ake bi wajen tantance cancantar shiga gasar, yayin da kungiyar kare muhalli ta FFF ta ce shawarar buga gasar a nahiyoyi uku barazana ce ga muhalli. Tuni dai a farkon watannan shugaban hukumar kwallon kafar Turai, Aleksander Ceferin ya bayyana matakin a matsayin ”mummunar shawara”.
Ya ce wannan shawara ta yiwu ta fi ba shi mamaki fiye da su, domin shi yana ganin wannan shawara ce maras kyau a ra’ayinsa. Za dai a fara gasar 2030 a Uruguay – kasar da ta fara lashe gasar a 1930, a wani bangare na bikin cika shekara 100 da fara gasar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp