Aminiya:
2025-04-01@03:06:36 GMT

Yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasuwannin Arewa

Published: 1st, March 2025 GMT

Farashin kayayyakin abinci kamar masara da shinkafa da gero da dawa da wake da gari da waken soya da dai sauransu sun ragu, musamman a manyan jihohin da ake nomawa, kamar yadda wani bincike da Aminiya ta gudanar ya nuna.

Wannan na faruwa ne gabanin watan Ramadan, wanda aka fara yau Asabar.

Yadda ake ‘Spring rolls’ Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a Borno

Haka kuma an ce, jihohin da ba sa noma suna jin tasirin rage farashin kayan abinci.

Masana sun danganta faduwar farashin da aka samu a kasuwa ga karancin kudi da kuma yadda aka yi bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara, wanda hakan ya haifar da faduwa farashin sosai.

Wasu kuma sun ce, yawan shigo da kayan amfanin gona da aka yi a baya-bayan nan shi ma ya taimaka wajen faɗuwar farashin.

Misali, buhun fulawa mai nauyin kilo 50, wanda ake sayar da shi kan Naira 80,000 a ’yan makonnin da suka gabata, yanzu ana sayar da shi ne tsakanin Naira 61,000 zuwa Naira 63,000 ya danganta da kasuwa.

Farashin hatsi ya ragu, sai dai na gyada da koko da dawa da dankalin Turawa da dabino da mai da kayan lambu sun dan yi tsada a kasuwanni da dama da wakilanmu suka zagaya.

Kaduna

A kasuwar hatsi ta Saminaka da ke Jihar Kaduna, buhun masara mai nauyin kilo 100 da ake sayar da shi tsakanin Naira 70, 000 zuwa Naiera 75,000 a mafi yawan kasuwanni a lokacin girbi, yanzu ya dawo Naira 47,000, yayin da waken soya da ake sayar da shi a baya a kan Naira 110,000, yanzu ya koma Naira 68,000.

Hakazalika, nau’in farin wake da ake sayar da shi kan Naira 150,000 a lokacin girbi, yanzu ya zama N100,000.

A kasuwar Giwa da ke Jihar Kaduna, ana sayar da gero da dawa tsakanin Naira 50, 000 zuwa Naira 51,000 sabanin Naira 79,000 zuwa N80,000 da aka sayar a bara.

Farashin wake ya fadi daga Naira 120,000 zuwa Naira 80,000; farin wake daga N160,000 zuwa Naira 88,000; irin shinkafa, Naira 75,000 zuwa tsakanin N55,000 zuwa N60,000.

Taraba

A kasuwar hatsi ta Mutum Biyu da ke Jihar Taraba, farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 100 a yanzu ya kai Naira 45,000 sabanin Naira 50,000 a watan da ya gabata; buhun masara mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi a baya a kan Naira 57,000, yanzu yana tsakanin Naira 40,000 zuwa N45,000; buhun rogo mai nauyin kilo 100, a baya Naira 25,000, yanzu ya zama Naira 18,000 da N19,000.

Binuwai

A Kasuwar Wadata da ke Makurdi a Jihar Binuwai, buhun shinkafa ta gida mai nauyin kilo 50 a yanzu ya kai Naira 26,000 zuwa Naira 29,000 sabanin Naira 45,000 zuwa Naira 55,000 da ake sayar da shi kimanin wata shida da suka wuce.

A Kasuwar Zamani, farashin laka na shinkafa ya ragu daga Naira 2,700 zuwa N1,800, kamar yadda Aminiya ta tattaro.

Haka kuma babban kwandon tumatur, wanda a baya ana sayar da shi kan Naira 45,000, yanzu haka yana kan Naira 30,000 zuwa Naira 35,000.

Farashin mudu na masara da gero da masarar Guinea ya fadi daga Naira 3,200 zuwa Naira 1,200; kwanon dabino, yanzu ya zama N1,800 daga Naira 2,500; robar garri Naira 2,300 daga Naira 3,500; doya 10 tsakanin Naira 10,000 zuwa Naira 15,000 daga tsakanin Naira 12,000 zuwa Naira 18,000.

Kano

A Jihar Kano ma wakilinmu ya ruwaito faduwar farashin kayan abinci. A kasuwar Danhassan, farashin kwano na wake ya ragu zuwa Naira 2,500 daga Naira 3,500; gero Naira 1,200 daga Naira 2,700.

A Kasuwar Dawanau, kwanon masara yanzu yana tsakanin Naira 1,200 zuwa Naira 1,300; gero, Naira 1,000 da Naira 1,100; wake tsakanin Naira 2,000 zuwa Naira 2,200 kowane mudu.

Neja

A kasuwar Manigi da ke Karamar Hukumar Mashegu a Jihar Neja, farashin buhun jan wake ya fadi daga Naira 200,000 zuwa Naira 90,000 daga Naira 200,000; sai farin wake ya koma Naira 90,000 daga N160, 000; inda farashin farar masara da ja ya koma Naira 40,000 a kowane buhu, maimakon Naira 85,000 da ake sayarwa a baya; gero a yanzu Naira 45,000 ne; dawa Naira 40,000; buhun wake Naira 78,000 sabanin Naira 135,000 a bara.

A Kasuwar Lemu, a halin yanzu ana sayar da buhun gero da masara da dawa kan Naira 42,000; da buhun shinkafa (nika) 100 kilo Naira 108,000.

A garin Bida, wani dan kasuwa, Mohammed Mahmud ya bayyana cewa, farashin shinkafa ’yar gida ya fadi daga Naira 130,000 zuwa Naira 120,000 kan kowane buhu.

Buhun dawa da gero yanzu ya zama Naira 45,000; masara Naira 48,000. A kasuwar karshen mako ta Gwadabe, wakilinmu ya ruwaito cewa, farashin shinkafa da masara da dawa ma sun fadi.

Gombe

A babbar kasuwar Gombe bangaren ’yan shinkafa da a kwanakin baya ake sayar da babban buhun shinkafar dafawa mai nauyin kilo 100 a kan farashi mabambanta bisa ga kyawun shinkafar da ya kai hawa uku na Naira dubu 180,000 da dubu dari 160,000 da dubu 150,000 yanzu haka farashin ya fadi.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kayan abinci Ramadan da ake sayar da shi ya fadi daga Naira 000 sabanin Naira 000 zuwa Naira tsakanin Naira yanzu ya zama zuwa Naira 1 ana sayar da Naira 45 000 daga Naira 2 a kan Naira

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo

’Yan Sanda sun kama mutum 14 da ake zargi da hannu a kisan matafiya 16 ’yan Arewa a kan titin Uromi zuwa Obajana, a Jihar Edo.

Sufeto-Janar na ’Yan Sanda (IGP), Kayode Egbetokun, ya yi tir da wannan hari, kuma ya bai wa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Hedikwatar Rundunar da ke Abuja, yin bincike.

Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja

Bayan faruwar lamarin, rundunar ’yan sandan Jihar Edo, ta tura jami’anta zuwa yankin domin wanzar da zaman lafiya.

Har ila yau, ana ci gaba da farautar sauran waɗanda suka tsere.

Kakakin rundunar ’yan sanda, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce Sufeto-Janar ya ba da umarnin a kamo waɗanda ke da hannu a lamarin.

Ya tabbatarwa da al’umma cewa ’yan sanda ba za su yarda da kisan gilla ba, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.

Sufeto-Janar ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu kuma su ba da haɗin kai wajen bincike.

Haka kuma, ya gargaɗi mutane kan ɗaukar doka a hannunsu, tare da tunatar da su cewa mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba laifi ne.

’Yan sanda sun kuma gargaɗi jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu, tare da kiran su da su riƙa kai rahoton duk wani abu da suka gani wanda ba su yarda da shi ga hukumomin tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan ‘Yan Arewa: Gwamnan Edo Ya Kai Ziyarar Jaje Kano
  • Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
  • YANZU-YANZU: Gwamnan Edo Ya Kai Ziyarar Jaje Kan Kisan Mafarauta A Uromi
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
  • Farashin fetur ya ƙaru sakamakon hana Dangote mai a Naira
  • Shin Mbappe Zai Iya Maye Gurbin Ronaldo A Real Madrid?
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Karrama Hakimai Da Limamai Da Kayan Sallah
  • Wadanda Iftila’in Tankar Mai Ya Sha A Jigawa Sun Sami Naira Miliyan 4 Kowannensu
  • Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)
  • Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo