Amma duk da haka, hatta wake-wake da raye-raye da kuma abinda ya shafi sinima, tsofaffin jarumai ne su ka kawo su a masana’antar Kannywood, saboda haka ya kasance wani lokaci mai ban sha’awa a tarihi lokacin da Hamisu Lamido Iyan-Tama ya hadu da Hindatu Bashir a kan dandamali don ba shi lambar yabo.

Dukkanmu sai muka tuna da fim dinsu na Badakala (wanda wani jarumi Bashir Mudi Yakasai ya shirya), inda suka yi fim mai dauke da rawa da waka na farko a cikin fina-finan Hausa,wato a shekarar 1997 wannan fim ya daga abinda yanzu ake kira Hausa Afropop, domin shi ne wakar fina-finan Hausa ta farko da aka kai wa Rabi’u BK a kasuwar Kofar Wambai domin sayar da shi a matsayin shirin waka mai zaman kansa, Dan Azumi Baba, wanda ya rubuta labarin, ya na nan tare da su a wannan babban taron.

Tsoffin jaruman Kannywood a bisa wata kungiya mai zaman kanta wadda akasari mata suka kafa wacce a yanzu na ke kira “Hausa Classic Cinema” karkashin jagorancin mutane irin su Wasila Isma’il, sun yanke shawarar gudanar da taron shekara-shekara domin yaba wa kansu da kuma wadanda suka bayar da gudunmawa wajen ci gaban masana’antar.

Ni dai ban san su ba, kuma Hindatu Bashir da ta shirya taron na shekarar 2025 sai da ta bi ta hannun mutane biyu domin su zo wurina su kawo mani goron gayyata, Hamisu Lamido Iyan-Tama ya kira ni ‘yan sa’o’i kadan kafin taron ya nemi in halarta, mutane biyu ne kacal a Kannywood da za su umarce ni da in yi irin wannan abu, kuma zan yi su ne Hamisu Iyan Tama da Alkanawy, da na shirya sai na tafi tare da dana Munzir.

Wadannan tsofaffin jarumai sun kasance fuskokin fina-finan Hausa na gargajiya da labarun soyayya, eh labarun soyayya da a kan iya samun rikice-rikice na cikin gida sanadiyar soyayya kuma a samu mafita cikin sauki ta hanyar salo daban-daban, ba tare da sun nuna wani abu na tsiraici ba saboda dukkansu sun mallaki hankalinsu tun kafin su shiga harkar, saboda haka dole ne su tsare mutuncin kansu da na iyalinsu.

Manyan dattawan jarumai da su ka halarci wannan taron a ranar akwai Ado Ahmad Gidan Dabino, Dan Azumi Baba, Balaraba Ramat Yakubu, Bala Anas Babinlata, Hamisu Lamido Iyan-Tama da sauran wadanda su ka kafa kuma su ka zage damtse wajen ganin masana’antar ta tsayu da kafafunta tun daga shekarun 1990 zuwa yanzu, dayan jinsin kuma akwai dattawan jarumai mata kamar ita kanta da ta shirya taron Hindatu Bashir, Hajara Usman, Hadiza Kabara, Ladin Cima, Maijidda Abbas, Rukayya Dawayya, da wasu da yawa da ba zan iya tunawa ba.

A bangaren mu da muke zaune a teburin manyan baki kuwa akwai Muhammadu Rabi’u Rikadawa, sai Dan Azumi Baba, ni kaina, Ado Ahmad, Hajiya Balaraba, Ladi Cima da Hajara Usman,na yi matukar farin ciki da kasancewa cikin wadannan yan wasan kwaikwayo da furodusoshi,dukkan wurin cike yake da mutane, har ba za mu iya ganin sauran wadanda ke zaune a wannan teburi na manyan baki ba, amma dai na san cewar su ma sun bayar da irin tasu gudunmawar wajen wannan babban aiki da aka faro shekaru fiye da Talatin da su ka wuce.

An bai wa Ado Ahmad Gidan Dabino lambar yabo ta “Trailblazer Award, a matsayin wanda ya share fage ga al’ummar da su ka shigo Kannywood ta hanyar wani shiri nasa mai suna “In Da So Da Kauna”, fim din ya fayyace irin nau’in soyayya tun daga farko,ya kuma hada da hakikanin tarihin rayuwar Hausawa tare da hasashen goben bahaushe wanda a wancan lokacin har littafi ya rubuta akan wannan makala.

An bai wa Dan Azumi lambar yabo ta “Star Producer Award” bisa la’akari da rawar da ya taka a masana’antar nishadin Hausa baki daya, tabbas hakane, domin shi ne ya gano Hamisu Lamido-Iyan-Tama, babban dan wasan kwaikwayo mai ban sha’awa wanda zai iya tsayuwa a duk inda wani jarumi ya tsaya ko da kuwa a masana’antar Hollywood ne.

Abin ban mamaki duka biyun Dan Azumi da Ado sun fara zama kwararrun marubutan Hausa kafin su yi kaura zuwa masana’antar fim a matsayin uwayen da su ka kafa ta, a tsakiyar shekarun 1990, a farkon shekarar 2000 an mayar da su zuwa matsayin mashawarta kawai, rawar da su ka taka a cikin manyan fina-finai na baya bayan inda Ado Ahmad ya fito a matsayin Gwamna (Kwana Casa’in) wanda shirin siyasa ne, da Dan Azumi a matsayin Kamaye a shirin Dadin Kowa, wanda akayi saboda hadin kan al’umma, ya nuna cewar DA TSOHUWAR ZUMA AKE MAGANI, don kuwa bani tunanin akwai wani daga cikin matasan jarumai na yanzu da zai yarda ya taka irin wannan rawar.

Balaraba Ramat Yakubu ta samu lambar yabo ta “Legendary Producer Award, inda aka karramata da lambar yabo ta furodusar da ta taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban masana’antar Kannywood, fina finanta irinsu Sai A Lahira” da “Alhaki Kwikwiyo” za su dade ana tunawa dasu a tarihin wannan masana’antar a kodayaushe, abinda na kira “Kannywood Classics”, Hamisu Lamido Iyan-Tama ya sami shaidar wani mutum da ya nunawa manyan gobe hanyar da ya kamata su bi a wannan masana’antar.

An ba ni lambar yabo ta “Special Recognition” a matsayin wadanda ba jaruman fim ba amma kuma su ka bayar da gudunmawarsu ta wata sigar, amma kuma sun cancanci karramawa saboda irin gudunmawar da suka bayar ta hanyar inganta da kuma kiyaye al’adun Hausa ta hanyar fim”, duk da cewar rukunin gajerun bidiyo ya kamata ace na fito amma dai wannan kyautar na dauke ta a matsayin karramawa ta musamman a wajena.

A kan dandamalin “Red Carpet”, an tambaye ni yadda na ji game da taron, sai na mayar da martani cewa taron ya fayyace ainahin abinda ake kira Da Tsohuwar Zuma Ake Magani, duba da dimbin taurarin da su ka halarci taron, wadanda su ne uwa da magoyiyar masana’antar nishadin zamani ta Hausa, wadannan taurari sun samar da fina-finai masu tsafta, wanda ake yaba wa kuma ana kiransu da ‘Classics’.

Sun gabatar da fina finai na Iyali da sauran abubuwan da su ka shafi rayuwar Malam Bahaushe, amma da wasu su ka zo sai suka yi watsi da wadannan fina finai suka kama wasu labaran karya game da Hausa da rayuwarsu, irin wadannan tsofaffin gwanaye wadanda ke da tsantsar sani na al’adar fina-finan Hausa ne za su kai ga farfado da fina-finan Hausa, su ne za su jagoranci hanyar kai masana’antar Kannywood zuwa Tudun Mun Tsira.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Farfesa Abdallah Kannywood Hamisu Lamido Iyan Tama a masana antar lambar yabo ta

এছাড়াও পড়ুন:

An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi

An shiga ruɗu da fargaba a garuruwan ƙasar Chadi da dama, sakamakon jita-jita da kafofin sada zumunta na yanar gizo ke yaɗawa cewa wasu matsafa na satar al’aurar maza.

Tun daga birnin Moundou da ke kudancin kasar da lamarin ya fara samun asali, inda wasu matasa hudu suka yi ikirarin cewa an sace musu al’aurarsu ta hanyar bakar tsafi, na yaduwa kamar wutar daji a wasu manyan biranen ƙasar Chadi.

Sakamakon jita-jita da bidiyoyi iri-iri da ake yadawa a shafukan sada zumunta, duk da cewa ba a tabbatar da wannan zargi a likitanci ko a hukumance ba, lamarin ya bazu tare da tada hankula har a tsakiyar N’Djamena, babban birnin kasar, inda wasu fusatattun mutane suka yi yunkurin kashe wani mutum wanda suka zarga da sace al’aurar wasu yara maza uku bayan ya yi musabaha da su, sai dai ya tsira da ransa sakamakon shiga tsakani da ’yan sanda suka yi, amma ya ji jiki da ɗan karen duka.

Babu tushe a zahiri

A yayin da ake fuskantar wannan al’amari wanda a halin yanzu girmansa na iya haifar da hargitsi na zaman lafiyar jama’a, gwamnati ta yanke shawarar tashi tsaye don ƙoƙarin kawo karshensa.

Kakakin gwamnatin Chadi, Gassim Cherrif ya ce lamarin na neman wuce gona da iri, domin kuwa ana kai wa mutane hari tare da jikkata da dama saboda zargi marasa tushe a zahari, yana mai cewa gwamnati ba za ta zuba ido tana gani har lamarin ya girma ba, ta yadda mutane ke ɗaukar doka da hannunsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza
  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • Zaɓen 2027: Me ya sa jam’iyyu ke neman tabarrakin Buhari?
  • Hamas ta yi watsi da shirin kwance damara na Isra’ila
  • An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 15 Na Birnin Beijing
  • An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi
  • Manyan jami’an gwamnati sun halarci auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi
  • Minista Ya Sake Jaddada Ƙudirin Sabunta Kayan Aikin Watsa Labarai Na Gwamnati
  • Ya kashe masoyin tsohuwar matarsa bayan sakinta a Neja