A jiya Juma’a ne mai magana da yawun ma’aikatar tsaron jama’a ta kasar Sin ya bayyana rashin amincewa da barazanar da Amurka ta yi ta sanya karin harajin kashi 10 cikin dari kan kayayyakin da kasar Sin ke fitarwa. Ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani ga wata tambayar manema labarai kan barazanar karin haraji da Amurka ta yi, wanda zai fara aiki daga ranar 4 ga Maris, kuma ta ambaci matsalar fentanyl a matsayin dalilin.

Kakakin ya ce, kasar Sin ta ba da goyon baya ga Amurka wajen tinkarar matsalar fentanyl bisa dalilan jin kai, kuma ta samu sakamako mai kyau. Ya kara da cewa, rikicin fentanyl matsala ce da tushenta ke cikin Amurka. Yana mai cewa, bangaren Amurka ya yi watsi da hakikanin gaskiya kuma ya kasa magance ainihin batutuwan da suka shafi bukatun miyagun kwayoyi yayin da yake dora laifin kan wasu kasashe. Abin da Amurka take yi ba zai taimaka wajen magance matsalar ba, kuma zai yi illa sosai ga hadin gwiwar Sin da Amurka kan yaki da muggan kwayoyi. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

New York Times : Amurka na son rage ofisoshin jakadncinta a Afirka

Wani rahoto da jaridar New York Times ta Amurka ta fitar ya nuna cewa Amurka na neman rage kasantuwarta a duk duniya musamman a Afirka.

Jaridar ta bayyana wani daftarin dokar shugaban kasa na sirri wanda ya tanadi “sake tsara tsarin ma’aikatar harkokin wajen Amurka.

Sai dai ministan harkokin wajen kasar Marco Rubio, ya musanta wadannan shirye-shiryen.

Batu na farko na shirin sake fasalin ma’aikatar harkokin wajen Amurka shi ne rage ofisoshin ma’aikatar harkokin wajen Amurka a bangaren sauyin yanayi, dimokuradiyya, da kare hakkin bil’adama, batutuwan da gwamnatin Trump ta shiga kafar wando guda dasu.

Rahoton ya ce rage kasafin kudin zai kai ga rufe ofisoshin jakadanci a kasashen waje,  amma inda Amurka za ta rage yawan aikin diflomasiyya shi ne a Afirka.

Domin Washington ta yi imanin cewa akwai yankuna hudu kawai a duniya inda kasancewarta zai kasance mai mahimmanci: Eurasia, Gabas ta Tsakiya, Latin Amurka da Asiya-Pacific.

Don haka Afirka Amurka za ta samar da jakada na musamman kan harkokin Afirka.” wanda zai kai rahoto ga Majalisar Tsaro ta Fadar White House, ba Ma’aikatar Harkokin Wajen ba.

Kudirin ya kuma bayyana cewa “za a rufe dukkan ofisoshin jakadanci da karamin ofishin jakadancin da ba su da mahimmanci a yankin Saharar Afirka.” A ƙarshe, duk sauran ayyukan da suka rage za a hada su karkashin ikon manzo na musamman.

An shirya aiwatar da wadannan sauye-sauye a ranar 1 ga Oktoba, a cewar jaridar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Shugaban Ma’aikatar Shari’a Yana Halartar Taro A Kasar China
  • Sin Na Hasashen Samun Karin Yabanya A Shekarar 2025
  • HOTUNA: An yi zanga-zangar adawa da matsalar tsaro a Filato
  • New York Times : Amurka na son rage ofisoshin jakadncinta a Afirka
  • Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI
  • Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI
  • Jakadan Sin A Amurka: Beijing Na Adawa Da Duk Wani Nau’in Karin Haraji Ko Yakin Ciniki
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar