Sin Ta Kiyaye Girmama Kasashen Tsibirai Na Yankin Tekun Pasifik
Published: 1st, March 2025 GMT
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taba jaddada cewa, kasar Sin ta girmama ikon mallakar kasa da cikakken yanki na kasashen tsibirai na yankin tekun Pasifik, da girmama bukatunsu da al’adun kabilunsu da kuma hadin gwiwarsu wajen samun ci gaba da kansu. A kwanakin baya, yayin da firaministan kasar tsibiran Cook Mark Brown yake hira da wakiliyar babban gidan rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG, ya bayyana cewa, Sin ta kiyaye girmama kasashen tsibirai na yankin tekun Pasifik a fannoni 4.
Firaminista Brown ya yi nuni da cewa, kasarsa ta tsibiran Cook ta dora muhimmanci ga girmamawar da Sin ta nuna mata, kasar Sin ta kiyaye yin hakan tun da aka kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu. A sakamakon girmama kasar tsibiran Cook da Sin ta yi, sauran kasashen duniya sun fara kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu da kasar tsibiran Cook. Kasar tsibiran Cook ta nuna godiya ga kasar Sin kan wannan batu, kuma ita ma tana girmama kasar Sin. Duk yadda kasa ta kasance babba ko karama, ya kamata kasashe su nuna girmamawa ga juna, hakan shi ne tushen raya dangantakar dake tsakaninsu. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasar tsibiran Cook
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar Yemen Zata Kakaba Takunkumi Kan Jiragen Saman Fasijan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Sojojin Yemen sun sanar da killace sararin samaniyar Falasdinawa da yahudawan sahayoniyya suka mamaye
Sojojin Yemen sun sanar a yammacin jiya Lahadi cewa: Za su kakaba wa haramtacciyar kasar Isra’ila cikakken takunkumi ta sama, yayin da kamfanonin jiragen sama na kasa da kasa suka yi gargadin hadarin da ke tattare da zirga-zirga daga filayen jiragen saman yankunan Falasdinawa da aka mamaye. Wannan dai na zuwa ne a matsayin martani ga karuwar hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai wa a zirin Gaza.
Kakakin rundunar sojin Yemen, Birgediya Janar Yahya Sari’e, ya ce za su kakaba takunkumin ne ta hanyar kai hare-hare akai-akai kan filayen jiragen saman haramtacciyar kasar Isra’ila, musamman filin jirgin sama na Ben Gurion.
Sanarwar ta yi gargadi ga dukkan kamfanonin jiragen sama na kasa da kasa kan hadarin da ke tattare da hakan, inda ta yi kira gare su da su “soke dukkan tafiye-tafiyen jiragen da ke zuwa filayen jiragen sama na gwamnatin ‘yan mamaya masu tafka muggan laifuka domin kare lafiyar jiragensu da na kwastomominsu.”
Birgediya Janar Sari’e ya jaddada cewa: Kasar Yemen ba za ta amince da ci gaba da keta hurumin da makiya ke kokarin aiwatarwa ta hanyar kai wa kasashen larabawa irinsu Lebanon da Siriya hari ba, yana mai jaddada cewa “wannan al’ummar ba za ta ji tsoron bullar duk wani fada ba, kuma za ta ki mika wuya da rusuna wa azzalumai.”