Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi watsi da shawarar da Isra’ila ta gabatar na tsawaita matakin farko na yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza, inda ta yi kira ga kasashen duniya da su matsa wa gwamnatin mamayar lamba don ci gaba da mataki na biyu na yarjejeniyar kamar yadda aka tsara tun farko.

Yau Asabar ne dai matakin farko na yarjejeniyar ke kaow karshe.

Kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem ya bayyana a wata hira da gidan talabijin na Al Araby cewa, ba za a amince da tsawaita matakin farko na yarjajjeniyar kuma gwamnatin mamaya na da cikakken alhakin gazawar fara shawarwari a mataki na biyu na tsagaita wuta a zirin Gaza.

Qassem ya kuma lura da cewa, maganar da Isra’ila ta yi na tsawaita kashi na farko na da nufin kwato sauran mutanen da aka yi garkuwa da su.

Ya ci gaba da cewa gwamnatin Isra’ila tana kaucewa kudurinta na kawo karshen yakin da kuma ficewa daga zirin Gaza gaba daya.

Qassem ya ci gaba da cewa, babu wata tattaunawa a halin yanzu na wani mataki na tsagaita bude wuta a Gaza da kungiyar Hamas, yana mai jaddada cewa dole ne a fara tattaunawa a mataki na gaba da nufin samar da tsagaita wuta ta dindindin.

Ya kuma bukaci masu shiga tsakani da kasashe masu bada garantin da su tursasa gwamnatin Isra’ila ta ci gaba da aiki da yarjejeniyar a dukkan matakanta, sannan ta shiga mataki na biyu ba tare da wani shakku ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Kara Kakabawa Saura Haraji—Matakin Farfado Da Masana’antun Amurka Ko Girbar Abin Da Take Shukawa?

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta kashe yara 322 cikin kwanaki 10 a Gaza — UNICEF
  • Sin Da Zambiya Sun Daddale Yarjejeniyar Fitar Da Kwarurun Macadamia Nuts
  • HKI Ta Sake Kai Wa Unguwar Dhajiya Dake Beirut Hari
  • Kara Kakabawa Saura Haraji—Matakin Farfado Da Masana’antun Amurka Ko Girbar Abin Da Take Shukawa?
  • Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris
  • Yawan Kayayyakin Da Aka Yi Hada-hadarsu A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Sin A 2024 Ya Ci Gaba Da Kasancewa Na Farko A Duniya
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne