HausaTv:
2025-04-21@13:24:43 GMT

Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa

Published: 1st, March 2025 GMT

Shugaban Ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya ce bai ga laifin da ya yi wa Shugaban Amurka Donald Trump, ballantana ya nemi afuwa.

Zelensky ya bayyana haka ne bayan zazzafar cacar-baki da ya kaure a tsakaninsa da Trump a ofishin shugaban ƙasar Amurka.

A cewarsa, “ina godiya ga Amurka da gudunmuwar da take ba mu,” in ji shi kamar yadda ya bayyana a hirarsa da Fox News.

Sai dai ya bayyana cewa musayar yawun ba ta dace ba, sannan ya kara da cewa dangantakar da ke tsakaninsa da Trump za ta gyaru.

Tunda farko dai an soke taron manema labarai da aka shirya yi a fadar White House a jiya Juma’a, inda shugaban Amurka Donald Trump da shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky suka shirya rattaba hannu kan yarjejeniyar ma’adinai tsakanin Amurka da Ukraine, bayan wani sa-in-sa mai zafi tsakaninsu biyun a ofishin Trump wato Oval office a safiyar ranar.

Bayan musayar yawun da aka yi a ofishin, Trump ya wallafa wata sanarwa a dandalin sada zumunta na Truth, yana mai cewa, “Na yanke shawarar cewa Shugaba Zelensky bai shirya ma zaman lafiya idan da hannu Amurka a ciki ba. Ya ci mutuncin kasar Amurka a cikin Oval office mai daraja. Zai iya dawowa idan ya shirya ma zaman lafiya.”

A nasa bangaren, Zelensky ya wallafa a dandalin sada zumunta na X cewa, “Zaman lafiya mai dorewa Ukraine ke bukata, kuma muna aiki don samun hakan.”

Haka zalika, shugabar Majalisar Tarayyar Turai Roberta Metsola ta bayyana a dandalin sada zumunta na X cewa, “Za mu ci gaba da yin aiki tare da kai don samun zaman lafiya mai dorewa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Bayyana Cikakken Ikon Tawagar Masu Tattaunawan Iran A Zaman Shawarwari Da Amurka

Mai ba da shawara ga Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Masu sasantawa Iran a birnin Roma suna da cikakken ikon gabatar da shawara kan matsayin kasarsu

Ali Shamkhani mai ba da shawara ga Jagoran juyin juya halin Musulunci ya yi nuni da cewa: Masu gudanar da shawarwari na Iran sun tafi birnin Roma ne domin yin shawarwari karo na biyu da Amurka kan batun makamashin nukiliyar kasar Iran. Ya ce masu yin shawarwari na Iran suna da cikakken ikon gabatar da shawara kan matsayin kasarsu.

Shamkhani ya yi nuni da cewa: Masu shiga tsakani na Iran suna neman cimma cikakkiyar yarjejeniya bisa ka’idoji guda tara: tsanani, samar da lamuni, dage takunkumi, yin watsi da tsarin Libya/UAE, kaucewa barazana, gaggauta yin shawarwari, dakile masu shirga karya kan Shirin makaman nukiliyar Iran -irin haramtacciyar kasar Isra’ila- da saukaka zuba jari. Iran ta zo ne domin cimma daidaiton yarjejeniya, ba ta mika wuya ga bakaken manufofin Amurka ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miji ya yi wa matarsa saki 3 a ofishin ’yan sanda
  • Gharibabadi : inganta sinadarin uranium jan layi ne a tattaunawar Iran da Amurka
  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Amurka : Ana ci gaba da zanga-zangar kyamar tsare -tsare da manufofin gwamnatin Trump
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma
  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Bayyana Cikakken Ikon Tawagar Masu Tattaunawan Iran A Zaman Shawarwari Da Amurka
  • News Fox: Sau 6  Yemen Ta Kakkabo Jiragen Amurka Samfurin Mq 9 A Karkashin Gwamnatin Trump
  • Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?
  • Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki
  • PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike