Wani jami’in ya ce yarjejejeniyar za ta ba da dama ga Zelenskyy da Trump su tattauna batun ci gaba da bayar da tallafin soji ga Ukraine, dalilin da ya sa Kyib ke son kammala yarjejeniyar.

Trump ya kwatanta wannan matsaya da aka cimma a matsayin “babbar yarjejeniyar,” wacce za ta kai ta tiriliyan na daloli.

A wani labarin kuma, Kasar Ukraine ta bayyana cewar hare-haren da Rasha ta kai wa garuruwan dake kusa da filin daga a gabashin kasar sun hallaka akalla mutum 5 tare da raunata wasu 8 ‘yan sa’o’i bayan wani mummunana harin jirgi mara matuki kusa da birnin Kyib.

Gagarumin ruwan wutar da jiragen saman Rasha marasa matuka suka kai cikin dare sun hallaka mutum 2 a kusa da birnin Kyib, ciki har da wata ‘yar jaridar Ukraine, kamar yadda kafar yada labaran da take yiwa aiki ta bayyana.

‘Yan jaridar dake yi wa kamfanin dillancin labarai na Afp aiki a Kyib sun ji karar fashewa bayan da rundunar sojin saman Ukraine ta ce Rasha ta yi barin wuta da jirage sama marasa matuka 177 masu nau’uka daban-daban kan wuraren da ta kai wa hari a fadin kasar.

Dakarun Rasha na kokarin kwace iko da garin Kostyantynibka kuma sun tsananta wajen yin luguden wuta akan sansanonin farar hula dake yankin gabashin Donetsk, wanda fadar Kremlin ke ikrarin cewa wani bangare ne na Rasha.

“An hallaka akalla mutum 5 kana an raunata wasu 8 a hare-haren da ake kai wa Kostyantynibka,” kamar yadda gwamnan yankin Donetsk Badim Filashkin ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

Hare-haren wata shaida ce ga karin wahalar da dakarun Ukraine ke sha a hannun rundunar sojin Rasha wacce ta ninkasu kudi da kayan aiki da kuma yawan dakaru a fadin fagagen daga.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ukraine

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha

Yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da Sergei Shoigu, sakataren majalisar tsaro ta kasar Rasha, a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar, Xi Jinping ya ce, Sin da Rasha sun kasance masu tuntubar juna a dukkan matakai, da aiwatar da matsayar da suka cimma da shugaba Putin da hadin gwiwa mai muhimmanci da moriyar juna tare da zurfafa hadin gwiwarsu a kai a kai, domin taimakawa muradunsu na bai daya na samun ci gaba da farfado da kasashen biyu. Ya kara da cewa, ya kamata kasashen 2 su karfafa hadin kai a harkokin da suka shafi yanki da ma duniya, su kuma goyi bayan rawar da kasashen BRICS da kungiyar hadin kai ta Shanghai suke takawa, tare da karfafa saita alkiblar hadin gwiwa da goyon bayan juna tsakanin kasashe masu tasowa.

A nasa bangare, Sergei Shoigu ya ce, Sin da Rasha sun kai wani matsayi da ba a taba gani ba, kuma ba su yi hakan don muzgunawa wata kasa ba. Ya ce, haduwar Sin da Rasha ta taka muhimmiyar rawa a duniya, kuma ta nuna misalin dangantaka tsakanin manyan kasashe. Ya ce, Sin da Rasha za su ci gaba da kasancewa masu aminci da juna da tattaunawa bisa daidaito, kuma muhimmin hadin gwiwar dake tsakaninsu, ya dace da muradunsu na bai daya. Bugu da kari, ya ce, Rasha za ta aiwatar da muhimman yarjejeniyoyin da shugabannin kasashen 2 suka cimma tare da karfafa dangantakarta da Sin. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 a ƙauyukan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 ƙauyukan Kebbi
  • Sojoji sun ƙwato makamai a dajin Sambisa
  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Sami Tarba Mai Kyau A Burtaniya Bayan Cacan Baki Mai Zafi Da Trump
  • Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa
  • Rasha Za Ta Bunkasa Kai Wa  Nahiyar Afirka Alkama
  • Kwastam Da Hukumar NPA Sun Kulla Hadakar Bunkasa Ingancin Aiki A Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha
  • An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya