Leadership News Hausa:
2025-04-02@15:54:44 GMT

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Published: 2nd, March 2025 GMT

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta gamu da cikas a kokarinta na darewa kan teburin gasar Laliga ta kasar Sifaniya, bayan rashin nasarar da ta yi a hannun Real Betis a filin wasa na Benito Villamarin da ke Seville.

Tsohon dan wasan Real Madrid, Isco Alacon ne ya lashe kyautar gwarzon dan wasa a wasan na ranar Asabar.

Isco ya na daya daga cikin ‘yan wasan da suka lashe kofin Turai biyar tare da Real Madrid.

Barcelona Na Cigaba Da Matsawa Real Madrid Lamba Mbappe Da Bellingham Ba Za Su Buga Wasan Da Real Madrid Za Ta Kara Da Leganes Ba

Real Madrid ce ta fara jefa kwallo ta hannun Brahim Diaz, kafin Johnny Cardoso ya farke wa masu masaukin bakin ana dab-da tafiya hutun rabin lokaci, Isco ya mayar da wasan danye bayan kwallon da ya jefa a minti na 54 da fara wasan.

Real Madrid wadda ke matsayi na biyu a gasar La Liga, sun buga wasanni 26, inda su ka samu nasara a wasanni 16, aka buga canjaras a wasanni 6, yayin da aka doke ta a wasanni 4.

Isco wanda ya shafe shekaru 9 a Santiago, ya jagoranci ‘yan wasan Betis a matsayin kyaftin a wasan na mako na 26.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

YANZU-YANZU: Gwamnan Edo Ya Kai Ziyarar Jaje Kan Kisan Mafarauta A Uromi

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Larijani Ya Ce Iran Zata Fara Kera Makaman Nukliya Idan An Kai Mata Hari Kan Shirin Ta Na Makamashin Nuliya
  • Allah Ya Yi Wa Galadiman Kano, Abbas Sanusi, Rasuwa 
  • Haaland zai yi jinyar mako bakwai — Guardiola
  • Tawagar Aikin Ceto Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin Ta Isa Myanmar
  • Kisan ‘Yan Arewa: Gwamnan Edo Ya Kai Ziyarar Jaje Kano
  • Shekaru 15, Wasanni 535, Yaushe Kane Zai Lashe Kofi A Ƙwallon Ƙafa?
  • YANZU-YANZU: Gwamnan Edo Ya Kai Ziyarar Jaje Kan Kisan Mafarauta A Uromi
  • An Fara Yakin Neman Zabe A Kasar Gabon
  • Iran Ta Zama Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Bakin Teku Karo Na 4 Asiya
  • Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda