An Kaddamar Da Taro Na 10 Na Zaunannen Kwamitin Majalisar CPPCC Karo Na 14
Published: 2nd, March 2025 GMT
An kaddamar da taro na 10 na zaunannen kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin wato CPPCC karo na 14 a yau 1 ga watan Maris a nan birnin Beijing, inda memban hukumar siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta Sin kuma shugaban majalisar CPPCC Wang Huning ya halarci taron.
A gun taron, an zartas da kudurin gudanar da zama na 3 na majalisar CPPCC karo na 14 a ranar 4 ga wannan wata a birnin Beijing, an kuma gabatar da shawara kan ajendar zaman, wato sauraro da yin bincike kan rahoton aiki na zaunannen kwamitin majalisar CPPCC da yadda aka gudanar da ayyukan da aka cimma daidaito a kai, a gun zama na 2 na majalisar CPPCC karo na 14, da halartar zama na 3 na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14, da kuma sauraro da tattaunawa kan aikin gwamnatin kasar da sauran rahotanni. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: CPPCC karo na 14 majalisar CPPCC
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta gargadi Amurka kan barazanar harin bam da Trump ya yi
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta gayyaci mai kula da harkokin kasar Switzerland da ke Tehran domin nuna fishi kan irin munanan ayyukan Isra’ila a yankin da kuma barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ke yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Babban daraktan ma’aikatar harkokin wajen Iran Issa Kameli ne ya gayyaci jami’in diflomasiyyar na Switzerland, wanda kasarsa ke wakiltar muradun Washington a Tehran, yau Litinin.
Kameli ya mika gargadin na Iran a hukumance ga wakilin kasar Switzerland dangane da duk wani aiki na barna tare da bayyana aniyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran na mayar da kakkausan martani cikin tsauri kan duk wata barazana.
Jami’in diflomasiyyar na Iran yayi tir da kalaman tunzura tashe-tashen hankula wandanda kuma suka sabawa dokokin kasa da kasa da kuma tsarin Majalisar Dinkin Duniya.
Wakilin na Switzerland ya ba da tabbacin cewa nan take zai isar da sakon Iran ga gwamnatin Amurka.
A ranar Asabar ne Trump ya ce za a kai wa Iran hari idan ba ta kulla yarjejeniya da Amurka ba.
“Idan ba su kulla yarjejeniya ba, za a ji bama-bamai,” in ji shi a wata hira da NBC News. Ya kuma yi barazanar ladabtar da Iran.