An Kaddamar Da Taro Na 10 Na Zaunannen Kwamitin Majalisar CPPCC Karo Na 14
Published: 2nd, March 2025 GMT
An kaddamar da taro na 10 na zaunannen kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin wato CPPCC karo na 14 a yau 1 ga watan Maris a nan birnin Beijing, inda memban hukumar siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta Sin kuma shugaban majalisar CPPCC Wang Huning ya halarci taron.
A gun taron, an zartas da kudurin gudanar da zama na 3 na majalisar CPPCC karo na 14 a ranar 4 ga wannan wata a birnin Beijing, an kuma gabatar da shawara kan ajendar zaman, wato sauraro da yin bincike kan rahoton aiki na zaunannen kwamitin majalisar CPPCC da yadda aka gudanar da ayyukan da aka cimma daidaito a kai, a gun zama na 2 na majalisar CPPCC karo na 14, da halartar zama na 3 na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14, da kuma sauraro da tattaunawa kan aikin gwamnatin kasar da sauran rahotanni. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: CPPCC karo na 14 majalisar CPPCC
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Jana’izar Shahidan Hizbullah Fiye Da 100 A Kudancin Lebanon
A jiya Juma’a ne dai aka yi jana’izar shahidan Hizbullah 130 a garuruwan Aytas-sha’ab da Aytarun da suke da kudancin Lebanon.
Tashar talabijin din al-manar ta watsa taron jana’izar shahidai 95 da su ka yi shahada watanni uku da su ka gabata a yayin yaki da HKI.
A garin Aytrun da shi ma yake a kudancin Lebanon an yi jana’izar shahidai 35.
Dukkkanin jana’izar biyu ta sami halartar dububan mutane daga cikin garuruwan da kuma wajensu.
A gefe daya, a daidai lokacin da ake gudanar da jana’izar mutanen a garin Aytatun, sojojin HKI sun kai hari a gefen garin, sai dai babu rahoto akan shahada ko jikkatar mutane.
Dan majalisa mai wakilntar Hizbullah a majalisar dokoki Hassan Fadlallah wanda kuma shi ne shugaban bangaren masu goyon bayan gwgawarmaya a majalisar, ya gabatar da jawabi a wurin jana’izar, inda ya bayyana cewa; Shahidan sun kwanta dama ne a fagen dagar kare daukakar al’ummar Lebanon.
A garin Aytas-sha’ab, an yi taho mu gama mai tsanani a tsakanin dakarun Hizbullah da sojojin mamayar HKI a lokacin yakin 2006, kuma a wannan yakin ma abinda ya faru kenan,’kamar yadda Fadlallah ya bayyana.
Dan majalisar ya kuma jaddada cewa; Za a sake gina wannan garin, kuma yin hakan nauyi ne da ya rataya a wuyan gwamnatin Lebanon.