Kasar Masar Ta Tabbatrawa Falasdinawa, Tana Bayansu Kafin Taron Kasashe Larabawa
Published: 2nd, March 2025 GMT
Gwamnatin kasar masar ta tabbatarwa gwamnatin Falasdinawa kan cewa tana goyon bayan falasdinawa a cikin dawo da hakkinsu, na kafa kasarsu mai cikekken yanci wacce take da gabacin birnin Qudus a matsayin babban birnin Kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Mostafa Madbouly ministan harkokin wajen kasar Masar yana fadar haka a lokacin ganawarsa da tokwaransa na gwamnatin Falasdinawa a Ramallah Mohammada Mustafa a birnin Alkahira.
Madbouly ya kara da cewa gwamnatin kasar Masar tana son ganin an gaggauta sake ginza Gaza da kuma maida rayuwa kamar yadda take a gaza da gaggawa.
Ya ce kasashen larabawa ba zasu taba yarda da kasar Falasdina kasa da yarjeniyar 4 ga watan Yunin shekara ta 1967.
A ranar Talata 4 ga watan Maris da muke ciki ne za’a gudanar da taron gaggawa na kungiyar kasashen larabawa a birnin Alkahira na kasar Masar don tattauna halin da Falasdinawa suke ciki musamman a Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Masar
এছাড়াও পড়ুন:
Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba
Shugaban majalisar mulkin kasar Sudan kuma kwamandan Sojin kasar Abdel Fattah al-Burhan ya tabbatar da cewa, farin cikin samun nasara a Sudan ba zai cika ba har sai an kawar da tungar karshe ta mayakan RSF a kasar, yana mai jaddada cewa kasar ba za ta ja da baya ba har sai an murkushe wadannan mayakan ‘yan tawaye, wadanda suka aikata munanan laifuka kan al’ummar Sudan.
Al-Burhan ya yi nuni da cewa, za a ci gaba da gwabzawa har sai an samu cikakken adalci, yayin da ya tabbatar da cewa ya tsaya tsayin daka da dukkan ‘yan kasar, kuma ya yi imani da ci gaba da kokarin maido da tsaro da kwanciyar hankali a kowane sako na kasar Sudan.
Al-Burhan ya ce: Har yanzu hanyar zaman lafiya da kawo karshen yakin a bude take, kuma duk wannan abu ne mai yiyuwa, kuma hanya a fili take, wato kungiyar RSF ta ajiye makamanta.
Ya tabbatar da cewa babu wata niyya ta tattaunawa da Rundunar ta RSF a yanzu, inda ya bayyana cewa kofar yin afuwa a bude take ga duk wanda ya ajiye makamansa. A ranar Asabar din da ta gabata ce sojojin kasar Sudan suka sake karbe ikon Kasuwar Libiya da ke yammacin birnin Omdurman, lamarin da ke nuna wani gagarumin mataki na ci gaba da suke samu, wanda ya biyo bayan sake kwac fadar shugaban kasa daga hannun dakarun RSF da sojojin na Sudan suka yi.