Gwamnatin kasar masar ta tabbatarwa gwamnatin Falasdinawa kan cewa tana goyon bayan falasdinawa a cikin dawo da hakkinsu, na kafa kasarsu mai cikekken yanci wacce take da gabacin birnin Qudus a matsayin babban birnin Kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Mostafa Madbouly ministan harkokin wajen kasar Masar yana fadar haka a lokacin ganawarsa da tokwaransa na gwamnatin Falasdinawa a Ramallah Mohammada Mustafa a birnin Alkahira.

Madbouly ya kara da cewa gwamnatin kasar Masar tana son ganin an gaggauta sake ginza Gaza da kuma maida rayuwa kamar yadda take a gaza da gaggawa.

Ya ce kasashen larabawa ba zasu taba yarda da kasar Falasdina kasa da yarjeniyar 4 ga watan Yunin shekara ta 1967.

A ranar Talata 4 ga watan Maris da muke ciki ne za’a gudanar da taron gaggawa na kungiyar kasashen larabawa a birnin Alkahira na kasar Masar don tattauna halin da Falasdinawa suke ciki musamman a Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Masar

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Papa Roma Farancis

A yau Litinin shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya fitar da sanarwa ta nuna aljinin rasuwar Papa Roma Farancis,sannan kuma ya mika sakon ta’aziyya ga Mabiya darikar Roman Katolika na duniya.

Shugaban kasar ta Iran ya rubuta cewa; Daga cikin matsaya da ta kasance fitacciya wacce Papa Roman ya dauka a lokacin rayuwarsa ita ce ta kalubalantar yadda ake take hakkin bil’adama a duniya, musamman mai dai yadda ya yi Allawadai da kisan kiyashin da ‘yan sahayoniya suke yi wa Falasdinawa a Gaza. Haka nan kuma yadda ya rika yin kira da HKI ta kawo karshen kisan kiyashin da take yi, da kashe mata da kananan yara.

Fizishkiyan ya kuma kara da cewa; Wadannan matakan da Papa Roman ya dauka a lokacin rayuwarsa za su wanzar da ambatonsa a cikin zukatan masu rayayyen lamiri da kuma wadanda suke yin kira da tabbatr da ‘yanci a duniya.

Shugaban kasar na Iran ta kitse sakon nashi da cewa; A madadin ni kaina da kuma  al’ummar Iran ina yin jinjina ga mamacin wanda ya yi fafutuka wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya.

A yau Litinin ne dai Fadar Vatican ta sanar da rasuwar Papa Roma Farancis wanda shi ne dan asalin yankin Latin na farko da ya jagoranci majami’ar .

Fadar ta kuma sanar da zaman makoki na kwanaki 9, sannan kuma ta sanar da cewa nan da makwanni biyu zuwa uku za a fara shirye-shiryen zabar sabon Papa Roma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Manufar Kasarsa Da Shirin Kare Muradunta A Duk Wata Yarjejeniya
  • Iran Ta Jaddada Matsayinta Kan Batun Tace Sinadarin Yuranium A Batun Tattaunawa Da Amurka
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Papa Roma Farancis
  • Hisbah ta kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi
  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • Kasar Rasha Ta Sanar Da Tsagaita Bude Wuta Da Ukraine Na Tsawon Kwanaki Bikin Ester
  • News Fox: Sau 6  Yemen Ta Kakkabo Jiragen Amurka Samfurin Mq 9 A Karkashin Gwamnatin Trump