Aminiya:
2025-04-24@18:08:10 GMT

Ban fitar da ran lashe Premier League na bana ba — Arteta

Published: 2nd, March 2025 GMT

Mikel Arteta ya ce, Arsenal ce za ta lashe kofin Premier League na kakar bana, ba kamar yadda ake hasashen Liverpool ba.

A ranar Laraba Gunners, wadda take da tazarar maki 11 tsakaninta da Liverpool za ta fafata da Nottingham Forest a wasan mako na 27 a Premier League.

Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta? An kama ɓarayin waya a Kano

A ranar Lahadin makon da ya gabata, Liverpool ta yi nasara a kan Manchester City da 2-0 a Etihad, bayan Arsenal ta yi rashin nasara 1-0 ranar Asabar a Emirates ta hannun West Ham.

Bayan wasan na West Ham Mikel Arteta ya zargi ‘yan wasan da rashin sa ƙwazo a fafatawar, bayan Gunners shafe kaka 21 rabon ta da kofin Premier League.

Kociyan ɗan kasar Sifaniya ya kara da cewa, ‘‘Damar ɗaukar babban kofin tamaula na Ingila na bana ba a hannuna yake ba.’’

To sai dai a shirin da Arsenal ke yi na karawa da Forest a ranar Laraba, Arteta ya ce, ba zai taɓa fitar da ran lashe kofin Premier na kakar bana ba.

Arsenal wadda take sa ran ɗaukar Premier na kakar bana ta gamu da koma-baya, saboda wasu ’yan wasanta da ke jinya.

Kai Havertz da Gabriel Jesus za su ci gaba da jinya har bayan kakar bana, ana sa ran Bukayo Saka zai koma taka leda a cikin watan Maris.

Rabon da Saka ya buga wa Arsenal tamaula tun cikin Disamba, shi kuwa Gabriel Martinelli na ci gaba da jinya.

Kyaftin Odegaard ya yi jinyar da bai buga wasa 12 ba tun farkon fara wasannin bana, inda kuma aka dakatar da wasu ’yan wasan Gunners.

’Yan wasa biyar na Arsenal aka bai wa jan kati a wasa 26 a Premier League kawo yanzu.

Arsernal ta daɗe tana biye da Liverpool a teburin Premier League, wanda tuni Gunners ta kai zagaye na biyu a Champions League, amma an yi waje da ita a FA da Carabao Cup.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arsenal Mikel Arteta

এছাড়াও পড়ুন:

Trump : “Mun yi ganawa mai kyau da Iran”

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana gamsuwarsa da yadda tattaunawa tsakanin kasarsa da Iran ke gudana, yana mai bayyana ta a matsayin mai matukar kyau.

Da yake magana da manema labarai a fadar White House jiya litinin, Trump ya ce tattaunawa da akayi da jami’an Iran sun yi matukar inganci.

A ranar 12 ga watan Afrilu ne aka gudanar da zagayen farko na tattaunawar wacce ba ta kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka a shiga tsakanin kasar Oman a birnin Muscat.

Haka zalika a ranar Asabar 19 ga watan Afrilu bangarorin sun yi wa ta biyu a birnin Rome na kasar Italiya, a shiga tsakanin kasar Oman.

kasashen biyu sun bayyana kwarin gwiwar cewa za a ci gaba da tattaunawa, inda za a sake gudanar da mataki na gaba a kasar Oman a ranar Asabar mai zuwa.

Kafin nan kwararu daga kasashen na Amurka da Iran zasu hadu a kasar Oman a gobe Laraba inda zasu tattauna game da shirin nukiliyar na Iran na zaman lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Sami Lambobin Yabo  8 A Wasan Taekwondo Na Duniya
  • CONMEBOL ta buƙaci a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta 2030
  • Hajjin Bana: Kamfanoni 4 da za su yi jigilar maniyyata — NAHCON
  • Manchester United Na Zawarcin Matheus Cunha Na Wolves
  • Za’a Yi Zana’izar Paparoma Francis A Ranar Asabar 26 Ga Watan Afrilu
  • Hargitsi A Filin Wasan Kwallon Kafa Tsakanin Al-Ahly Tripoli Da Al-Suwaihli A Kasar Libiya
  • Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran
  • Trump : “Mun yi ganawa mai kyau da Iran”
  • Kungiyar kare farar hula ta Falasdinu ta zargi sojojin da ” kashe-kashe masu yawa”
  • Darajar Cinikin Sarin Kaya Da Sayen Kayan Masarufin Sin Ta Karu Da Dala Biliyan 452.5 a Rubu’In Farkon Bana