Ban fitar da ran lashe Premier League na bana ba — Arteta
Published: 2nd, March 2025 GMT
Mikel Arteta ya ce, Arsenal ce za ta lashe kofin Premier League na kakar bana, ba kamar yadda ake hasashen Liverpool ba.
A ranar Laraba Gunners, wadda take da tazarar maki 11 tsakaninta da Liverpool za ta fafata da Nottingham Forest a wasan mako na 27 a Premier League.
Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta? An kama ɓarayin waya a KanoA ranar Lahadin makon da ya gabata, Liverpool ta yi nasara a kan Manchester City da 2-0 a Etihad, bayan Arsenal ta yi rashin nasara 1-0 ranar Asabar a Emirates ta hannun West Ham.
Bayan wasan na West Ham Mikel Arteta ya zargi ‘yan wasan da rashin sa ƙwazo a fafatawar, bayan Gunners shafe kaka 21 rabon ta da kofin Premier League.
Kociyan ɗan kasar Sifaniya ya kara da cewa, ‘‘Damar ɗaukar babban kofin tamaula na Ingila na bana ba a hannuna yake ba.’’
To sai dai a shirin da Arsenal ke yi na karawa da Forest a ranar Laraba, Arteta ya ce, ba zai taɓa fitar da ran lashe kofin Premier na kakar bana ba.
Arsenal wadda take sa ran ɗaukar Premier na kakar bana ta gamu da koma-baya, saboda wasu ’yan wasanta da ke jinya.
Kai Havertz da Gabriel Jesus za su ci gaba da jinya har bayan kakar bana, ana sa ran Bukayo Saka zai koma taka leda a cikin watan Maris.
Rabon da Saka ya buga wa Arsenal tamaula tun cikin Disamba, shi kuwa Gabriel Martinelli na ci gaba da jinya.
Kyaftin Odegaard ya yi jinyar da bai buga wasa 12 ba tun farkon fara wasannin bana, inda kuma aka dakatar da wasu ’yan wasan Gunners.
’Yan wasa biyar na Arsenal aka bai wa jan kati a wasa 26 a Premier League kawo yanzu.
Arsernal ta daɗe tana biye da Liverpool a teburin Premier League, wanda tuni Gunners ta kai zagaye na biyu a Champions League, amma an yi waje da ita a FA da Carabao Cup.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arsenal Mikel Arteta
এছাড়াও পড়ুন:
An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya
Hukumomi a Ƙasar Saudiyya, sun tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan da yammacin yau Juma’a.
Hakan na nuni da cewa azumin bana zai fara a ranar Asabar, 1 ga watan Maris, 2025.
Shafin Haramain Sharifain ne, ya tabbatar da wannan sanarwa, yayin da aka ga jinjirin watan a wurare daban-daban na ƙasar.
Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan KanoWannan na nufin cewa Musulmai a Saudiyya za su fara azumi a ranar Asabar.
Hakazalika, ƙasashen Qatar da Oman sun sanar da cewa za su fara azumin Ramadan a wannan ranar Asabar.
A yayin da ake shirin shiga wannan wata mai alfarma, an yi kira ga Musulmai da su yi amfani da lokacin azumi wajen ƙara yawan ibada, yin kyawawan ayyuka, da taimaka wa marasa galihu, duba da yanayin tattalin arziƙin duniya.
Ana sa ran cewa, Saudiyya da wasu ƙasashe, za a fara azumin Ramadan a sassa daban-daban na duniya a ranar Asabar, 1 ga watan Maris, 2025.