Aminiya:
2025-04-02@20:28:24 GMT

Kare ya ta da gobara a gida

Published: 2nd, March 2025 GMT

A wani bidiyo mai ban mamaki da Hukumar Kashe Gobara ta yankin Tulsa da ke kasar Amurka ta fitar ya nuna yadda wani kare ya yi sanadin tashin wuta a wani gida ta hanyar tauna fakitin batirin Lithium.

Hukuma ta kama karen bayan gano hakan a bidiyon mai ban mamaki, wanda ya nuna shi yana tauna fakitin batirin lithium-ion wanda mai shi ya bari.

Ban fitar da ran lashe Premier League na bana ba — Arteta Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta?

Bayan dan lokaci da fara taunawa, baturin ya fara tarwatsin wuta, sannan ya yi bindiga, lamarin da ya sa karen da wata kyanwa da ke kwana a kusa da gidan tserewa don tsira da rayukansu.

An yi sa’a, duk dabbobin sun tsere ta kofar gidan, wutar ba ta yi musu lahani ba, amma gobarar ta yi mummunar barna a gidan.

Masu kashe gobara a yanzu suna amfani da bidiyon a matsayin gargaɗi game da barin batir lithium a wurin da yara da dabbobi za su iya kaiwa.

Mai magana da yawun Ma’aikatar Kashe Gobara ta Tulsa ya ce, duk da irin barnar da gobarar ta yi, abubuwa na iya zama mafi muni idan akwai mutane da ke kwana a ciki, ko kuma yadda za a iya tsira da dabbobi marasa galihu.

“Lokacin da wannan wutar batirin ta fara ba tare da katsewa ba, ta haifar da zafi da samar da iskar gas mai konewa da guba har ma da tartsatsi,” in ji daya daga cikin ma’aikatar kashe gobaran, Andy Little game da makamashin da yake cikin kananan baturan lithium.

Ya ce, “Yana da mahimmanci ku bi ka’idojin masana’anta lokacin amfani da baturan lithium-ion, kawai amfani da caja da aka yarda da su da adana su a wajen da yara da dabbobin gida.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Kare

এছাড়াও পড়ুন:

Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar, ta ce taron barka da sallah da ta yi a mazaɓarta a yammacin Talata duk da haramta taruka da gwamnatin jihar ta yi ba karya doka ba ne.

Ana iya tuna cewa Gwamnatin Kogin dai ta hana duk wani nau’in taro ko gangami a jihar, saboda dalilin da ta ce na tsaro ne.

Haaland zai yi jinyar mako bakwai — Guardiola HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah

Kwamishinan ‘Yan sandan jihar, Miller Ɗantawaye, ya ce hana taron ya biyo bayan bayanan sirri da suka samu cewa za a samu barzanar tsaro, wanda ya tilasta gwamnatin jihar ɗaukar matakin.

Sai dai Natasha wadda ta isa jihar a wani jirgi mai saukar ungulu, ta bayyana wa magoya bayanta cewa tana da ’yancin kasancewa da mutanenta ta kuma yi shagalin farin ciki tare da su.

“A duk abin da za mu yi, mu sanya Allah a farko kuma mu shigar masa da buƙatunmu ta hanyar addu’a.

“Mijina ya kasance ɗaya daga cikin addu’o’ina da Allah Ya amsa. In banda haka ta yaya ni da ba kowa ba ce fa ce talaka daga ƙabilar Ebira na samu ƙarfin samun jirgin da zai kawo ni gida?

“Goyon bayan mijina ne ya kawo haka, kuma shi ke ciyar da ni gaba a koda yaushe.

“Tun jiya da na samu labarin za a rufe hanyoyi, aka kuma haramta taruka da jerin gwanon motoci a cikin gari na san cewa mu ne ake so a muzgunawa.

“Amma sai na faɗa wa kaina ai ba kakar siyasa ko yaƙin neman zaɓe ba ne yanzu.

“Don haka ni ba yaƙin neman zaɓe zan yi ba. Ni kaɗai ce zan shigo gari cikin mutane na, na yi shagalin bikin Sallah tare da su.

“Don haka babu wani laifi a ciki, babu dokar da na karya. A Najeriya muke. Ina da ’yancin shiga taruka da bukukuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Larijani Ya Ce Iran Zata Fara Kera Makaman Nukliya Idan An Kai Mata Hari Kan Shirin Ta Na Makamashin Nuliya
  • Duk Da Hanin Gwamna Da ‘Yansanda, Natasha Ta Isa Gida Kuma Ta Yi Taro
  • Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha
  • Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha
  • Kasar Sin Ta Nanata Adawa Da Matakan Tilastawa Da Nuna Babakeren Tattalin Arziki
  • Muna so a nuna wa duniya mutanen da suka kashe ’yan Arewa a Edo — Gwamnan Kano
  • Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Hadin Gwiwar Inganta Amfani Da AI Don Amfanar Da Kowa
  • An Fara Yakin Neman Zabe A Kasar Gabon
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda