Shugaban kasar Ukrain Volodomyr Zelesky ya samu tarba mai kyau a kasar Burtaniya bayan ya isa birnin London a jiya Asabar kuma bayan cacan baki mai zafi da yayi da shugaban Amurka Donal Trump a fadar White House dangane da yakin Ukraine.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya bayyana cewa shugaba Zeleski ya gana da firaiministan kasar Burtania Keir Starmer, wanda ya yaba masa kan yadda ya tsayawa kasarsa da kuma kasashen turai a gaban shugaban Amurka Donal Trump da mataimakinsa a ranar jumma’an da ta gabata.

Labarin ya kara da cewa shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya zanta da shuwagabannin biyu, wato Trump da kuma Zeleski don kwantar da hankali.

A yau Lahadi ce za’a gudanar da taro na musamman kan abinda ya faru tsakanin Zelesky da Trump da kuma makoman kasar Ukraine a yakin da take fafatawa da Rasha tun shekaru 3 da suka gabata.

Sauran shuwagabannin kasashen Turai sun yabawa Zelesky da yadda ya tsayawa kasarsa da kasa kasashen turai a tattaunawarsa mai zafi da manya-manyan Jami’an gwamnatin Amurka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha

Yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da Sergei Shoigu, sakataren majalisar tsaro ta kasar Rasha, a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar, Xi Jinping ya ce, Sin da Rasha sun kasance masu tuntubar juna a dukkan matakai, da aiwatar da matsayar da suka cimma da shugaba Putin da hadin gwiwa mai muhimmanci da moriyar juna tare da zurfafa hadin gwiwarsu a kai a kai, domin taimakawa muradunsu na bai daya na samun ci gaba da farfado da kasashen biyu. Ya kara da cewa, ya kamata kasashen 2 su karfafa hadin kai a harkokin da suka shafi yanki da ma duniya, su kuma goyi bayan rawar da kasashen BRICS da kungiyar hadin kai ta Shanghai suke takawa, tare da karfafa saita alkiblar hadin gwiwa da goyon bayan juna tsakanin kasashe masu tasowa.

A nasa bangare, Sergei Shoigu ya ce, Sin da Rasha sun kai wani matsayi da ba a taba gani ba, kuma ba su yi hakan don muzgunawa wata kasa ba. Ya ce, haduwar Sin da Rasha ta taka muhimmiyar rawa a duniya, kuma ta nuna misalin dangantaka tsakanin manyan kasashe. Ya ce, Sin da Rasha za su ci gaba da kasancewa masu aminci da juna da tattaunawa bisa daidaito, kuma muhimmin hadin gwiwar dake tsakaninsu, ya dace da muradunsu na bai daya. Bugu da kari, ya ce, Rasha za ta aiwatar da muhimman yarjejeniyoyin da shugabannin kasashen 2 suka cimma tare da karfafa dangantakarta da Sin. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Jana’izar Shugaban Kasar Namibia Da Ya Samo Mata ‘Yanci
  • Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Iran Ta Zama Zakara A Damben Gargajiya Ta 2025 UWW Wanda Aka Gudanar A Kasar Albaniya
  • Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House
  • Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha
  • Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano
  • Shugaban kasar Guinea-Bissau a ya yi wata ganawa da shugaban kasar Rasha