HausaTv:
2025-04-02@15:17:23 GMT

Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida

Published: 2nd, March 2025 GMT

Rahotanni da suke fitowa daga Nijar sun bayyana cewa; Wata kungiyar mai alaka da al-ka’ida ta  dauki alhakin kashe sojojin kasar 11 a kan iyaka da Aljeriya.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne dai lamarin ya faru,kuma a jiya Asabar ne aka yi jana’izarsu a garin Agadez, kamar yadda wata majiyar watsa labara ta jamhuriyar Nijar ta ambata.

Shafin “Air Info” da ya watsa laabrin ya kuma ce; Jami’an soja da dama sun hjalarci jana’izar sojojin da su ka kwanta dama, daga cikinsu har da janar Musa Salih Barmo, babban hafsan hafsoshin sojan kasar.

Tashar Radiyo din kasar ta Nijar ta ce, an yi wa sojojin kwanton bauna ne a lokacin da suke sintiri akan  mahadar iyakaokin kasar, da Mali da kuma Burkina Faso.

Labarin Radiyon ya kuma ce, Janar Barmo ya nufi asibitin garin Agadez din domin yin dubiyar sojojin da su ka jikkata.”

 A gefe daya wata kungiyar mai  suna; “Nasratul-Islam Wal Muslimin” da reshe ne na alka’ida, ta dauki alhakin kai harin.

A lokuta da dama a baya sojojin na jamhuriyar Nijar sun sha fuskantar hare-hare irin wadannan, sai dai ba kasafai kungiyoyin da suke ikirarin jihadi suke daukar alhakin kai wa ba.

Saharar dake Arewacin Nijar tana da girma kuma tana kusa da kasar Libya da masu hada-hadar mutane da kuma  ‘yan hijira suke bi suna ratsawa domin shiga cikin kasashen turai.

Kungiyar “Ikilid” wacce ba ta gwamnati ba da take sa ido akan duk wasu rikice-rikice da suke faruwa a duniya, ta ce daga 2023 zuwa yanzu an kashe mutane 2400 a cikin wannan kasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su

Mai martaba Sarkin zazzau,kuma shugaban majalisar sarakunan jihar kaduna, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya bukaci Dagatan da ke masarautar zazzau da su rinka sanya ido sosai akan zirga-zirgar bakin fuskokin da ba su gane ba a cikin su.

Ya yi kiran ne a sakon sa na sallah bayan kammala azumin watan Ramadan a fadar sa dake Zaria.

Ahmed Nuhu Bamalli ya bayyana cewa harkar tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a hakki ne na kowa amma ba gwamnati ita kadai ba,a don haka akwai bukatar ganin an hada karfi da karfe domin samun nasara a game da tsaron.

Mai martaba Sarkin ya kuma bukaci Dagatan da su rinka kai rahoton zuwan duk wani bako ko bakuwa da kuma dalilin zuwan.

Ya ce idan har aka dauki wannan matakin matsalar tsaro za ta ragu sosai,yana mai nuni da cewa sarakunan gargajiya na da muhimman rawar da za su taka game da tsaro.

Haka kuma Sarkin na zazzau ya bukaci iyaye da su rinka sanya ido game da harkokin yau da kullum na ‘ya’yan su.

Haka kuma ya gode wa gwamnan jihar kaduna da shugaban majalisar wakilai,Dr Abbas Tajuddeen, Iyan zazzau saboda irin aiyukan ci gaban da suke samar wa talakawa a zaria da sauran kananan hukumomin jihar kaduna.

A wani labarin kuma,Limamin masallacin juma’a na rukunin kananan gidajen dake kofar Gayan,Zaria, Sheikh Dalhatu Bello Amaru ya yi Allah wadai da kisar Gilla da wasu yan ta’adda suka yi wa wasu mafarauta yan arewa su 11 a Uromi da ke jihar Edo.

Ya yi Allah wadan ne a hudubar sa ta sallar idin karamar sallah da ya gudanar.

Ya ce mutanen Arewa ba su amince da kisar gillar da aka yi wa maharban ba gaira ba dalili.

Sheikh Bello Amaru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihar Edo da su tabbatar da ganin an kamo duk mutanen da suka aikata laifin domin suma a kashe su domin ran su bai fi na mafarautar da suka kashe ba tare da wani dalili ba.

Ya yi Bayanin cewa Allah ya bada umurnin cewa duk wanda ya kashe wani shima a kashe shi,amma hakan bai bada damar wani ya dsuki doka a hannun shi ba,hakki ne na hukumomin da abin ya shafa.

Haliru Hamza

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Yemen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kataparen Jirgin Ruwan Yaki Mai Daukar Jirage Na kasar Amurka
  • Sojojin Yemen Sun Harbo Jirgin Leken Asirin Amurka Samfurin MQ9
  • HKI Ta Sake Kai Wa Unguwar Dhajiya Dake Beirut Hari
  • Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF
  • Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka
  • Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya
  • Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su