HKI Ta Yi Barazanar Shiga Rikicin Da Ya Barke A Garin Jarmana Na Kasar Syria
Published: 2nd, March 2025 GMT
Kafafen watsa labarun HKI sun sanar da cewa sojoji a shirye suke su shiga cikin rikicin da ya barke a garin Jarmana dake kusa da birnin Damascuss na kasar Syria domin kare ‘yan Duruz.
Ofishin Fira ministan HKI Benjemine Netanyahi ya fitar da sanarwa a jiya Asabar da marece, yana ce; Netanyahu da ministansa na yaki Yesra’il Kats sun bayar da umarni ga sojojin kasar da su kasance cikin shiri domin kare ‘yan Duruz a garin Jarmana dake bayan binin Damascuss.
Ofishin watsa labarai na ministan yakin na HKI ya ce; Nauyi ne a wuyanmu mu kare ‘yan’uwanmu Duruz a cikin Isra’ila, da kuma hana a cutar da su a cikin Syria, don haka za mu dauki duk wani mataki da ya dace domin kare tsaronsu.”
Bayan kashe jami’an tsaron kasar Syria biyu, jami’an tsaron sun shiga cikin garin domin neman masu laifi,lamarin da ya haddasa taho-mu gama da makamai.
Kamfanin dillancin labarun Reuters, ya bayyana cewa; HKI ta bukacin Amurka da ta daina yin matsin lamba ga Rasha ta bar Syria saboda ta kalubalanci kwadayin Turkiya na shimfida nata ikon a wannan kasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar
“Mun zo nan ne a madadin gwamnatin tarayya domin ganowa da kuma jajanta muku rashin da aka yi, muna so mu tabbatar muku da cewa jami’an tsaro za su kawo karshen wannan kashe-kashen na rashin hankali.
“An yi mini cikakken bayani, kuma ina so in tabbatar muku cewa mun fahimci tushen wannan batu. Zamu kama wadanda suka aikata wannan aika-aika.
“Shugaban kasa ya damu matuka, kuma ya umarce mu da mu nemo wadanda suka aikata wannan aika-aika domin su fuskanci shari’a, muna aiki tare da gwamnatin jihar domin daukar tsarin da zai hana faruwar wannan mummunan lamari, lokaci ya yi da za a kawo karshen wannan hauka,” inji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp