HKI Ta Yi Barazanar Shiga Rikicin Da Ya Barke A Garin Jarmana Na Kasar Syria
Published: 2nd, March 2025 GMT
Kafafen watsa labarun HKI sun sanar da cewa sojoji a shirye suke su shiga cikin rikicin da ya barke a garin Jarmana dake kusa da birnin Damascuss na kasar Syria domin kare ‘yan Duruz.
Ofishin Fira ministan HKI Benjemine Netanyahi ya fitar da sanarwa a jiya Asabar da marece, yana ce; Netanyahu da ministansa na yaki Yesra’il Kats sun bayar da umarni ga sojojin kasar da su kasance cikin shiri domin kare ‘yan Duruz a garin Jarmana dake bayan binin Damascuss.
Ofishin watsa labarai na ministan yakin na HKI ya ce; Nauyi ne a wuyanmu mu kare ‘yan’uwanmu Duruz a cikin Isra’ila, da kuma hana a cutar da su a cikin Syria, don haka za mu dauki duk wani mataki da ya dace domin kare tsaronsu.”
Bayan kashe jami’an tsaron kasar Syria biyu, jami’an tsaron sun shiga cikin garin domin neman masu laifi,lamarin da ya haddasa taho-mu gama da makamai.
Kamfanin dillancin labarun Reuters, ya bayyana cewa; HKI ta bukacin Amurka da ta daina yin matsin lamba ga Rasha ta bar Syria saboda ta kalubalanci kwadayin Turkiya na shimfida nata ikon a wannan kasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji
Jami’an tsaro sun bazama akan titunan manyan garuruwan kasar Zimbabwe domin dakile zanga-zangar da ake shirin yi domin yin kira ga shugaban kasa Emmerson Mnangagwa ya yi murabus.
Tsofaffon sojoji da mayakan da su ka samarwa kasar ‘yanci ne dai suka yi kiran a yi zanga-zangar, saboda kin amincewa da shirin shugaban kasar na tsawaita wa’adin mulkinsa.
A cikin watan Janairu na wannan shekarar ne dai jam’iyyar ZANU-Party, mai mulki a kasar ta sanar da cewa tana son Mnangagwa ya ci gaba da rike mukamin shugaban kasar har zuwa 2023.
Mnangagwa dai ya hau karagar mulkin kasar ta Zimbabwe ne tun a 2017,bayan sauke Robert Mugabe daga kan karagar mulki cikin ruwan sanyi.
Shugaban mayakan nemawa kasar ‘yanci Blessed Geza ya zargi shugaban kasar da cin hanci da rashawa da kuma yi wa kujerar mulki rikon danko.
Shugaban kasar ta Zimbabwe dai ya sha bayyana cewa, ba ya da nufin tsawaita lokacin shugabancinsa.
Kundin tsarin mulkin Zimbabwe wanda aka rubuta a 2013 ya kayyade wa’adin shugabancin kasar na shekaru biyar sau biyu.