Burina in yi fice kamar mahaifiyata — Maryam ‘Yar Auta
Published: 2nd, March 2025 GMT
Maryam Abubakar sabuwar jaruma ce a Masana’antar Kannywood ’yar Hajiya Hauwa Garba da aka fi sani da ’Yar Auta ko Sabirar Gidan Badamasi.
A zantawarta da Aminiya ta ce babban burinta shi ne ta yi fice da suna kamar yadda mahaifiyarta Hajiya Hauwa Garba ta yi:
Mene ne takaitaccen tarihinki?
Sunana Maryam Abubakar wadda aka fi sani da Maryam Intete.
Yaya aka yi kika tsinci kanki a Masana’antar Kannywood?
Eh, ina harkar fim yanzu kuma zan iya cewa ina cikin wadanda suka fara tunda kuruciyarsu.
Na taso na ga yadda mahaifiyata take yi ne, shi ya sa ni ma na ce ina da sha’awar shiga harkar don in bayar da tawa gudunmawar.
Wane buri kike da shi tun kina karama?
Insha Allah zan ci gaba da karatuna don yanzu haka ina kokari ci gaba da karatu domin kwarewa a wani fannin daban bayan fim.
Shin kin haɗu da wasu matsaloli da kika fara fim?
Gaskiya ban haɗu da wata matsala ba, don ina yin wasu ’yan abubuwa haka ina ɗora wa a shafina na TikTok, wasu na yi min magana suna cewa gara ki hakura da fim ki yi aure. Ni kuma sai in ce musu aure lokaci ne insha Allahu zan yi idan lokacin ya zo.
Waɗanne abubuwa kike ganin ba haka kika zata ba a Kannywood?
Gaskiya idan zan iya bayar da shawara, idan mutum bai iya abu ba, yana da kyau ka zaunar da shi ka fahimtar da shi ko kuma idan an kawo maka kushe misali a ce idan ka zauna da mutum ka ji mene ne dalili?
Kada ka yanke hukunci nan take ba tare da jin ta bakinsa ba. Yanke hukunci lokaci daya babu kyau.
Mu ’yan Adam ne muna saba wa junanmu wani abin ma ai ba ka yi ba sai a je wajen ubangidanka a ce ka yi wani abu alhali ba ka yi ba. To wannan ne gaskiya nake ba manyanmu shawara su rika jin ta bakinmu idan an kawo musu kushe.
Mene ne burinki a masana’antar?
Ina fatar abubuwa da yawa. Na farko ina so in ga na yi suna kamar yadda mahaifiyata Hajiya Hauwa Garba ta yi.
Na biyu ina so in shahara a duniyar fim baki ɗaya.
Wane fim kika fi son fitowa a ciki?
Yanzu ka ga da Chamama da Barkwanci duk sun haɗu ba a gane kowane ɓangaren.
Ina hadawa ne, amma ba na yin kwalliya irin ta mahaifiyata.
A cikin finafinan da kika fito, wanne ya fi burge ki?
Akalla dai na yi finafinai da dama, amma uku sun fi fice saboda ban dade ba a masana’antar. Amma a ciki wanda ya fi burge ni shi ne Naja’atu.
Wadanne nasarori kika samu?
AlhdulilLahi na samu nasarori da dama. A ce mutum ya yi fice a san shi ma ai wani abu ne.
Nasarata ta farko da na samu zuwa na aikin Saudiyya na ga mutane da yawa sun san ni da suka gan ni, na ji matukar farin cikin yadda suke nuna ni. Wannan kadai ma nasara ce.
Wasu za su so sanin dalilin da ya sa kika haɗa sana’a da mahaifiyarki?
Ban ga abin mamaki ba, saboda tun ina yarinya mahaifiyata take harkar fim, wanda hakan ya sa na saba ganin yadda take yi. Wannan ya sa ko da na shigo ban sha wahala ba.
Kin fuskanci ƙalubale ko turjiya ta wajen mahaifi kan wannan harka?
Eh, mahaifina da farko ya ce min ba ya son harkar fim, ya fi son in yi aure, amma da na zauna muka fahimci juna da shi sai ya ce min shi ke nan babu damuwa Allah Ya taimaka.
Sakonki ga masu bibiyar finafinanki da masoyanki?
To sakona gare su shi ne su ci gaba da yi min addu’a Ubangiji Allah Ya kai ni gabar da nake son kaiwa. Ina godiya gare su. Allah Ya bar zumunci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hauwa Garba Maryam Abubakar
এছাড়াও পড়ুন:
Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da ‘yanci daga wuta
Azumin watan Ramadan na daga cikin shika-shikan Musulunci, kuma Allah ne Ya wajabta shi a kan bayinsa.
Wannan wata yana da falala da lada mai yawa, domin Allah Ya keɓe shi da girma da ɗaukaka.
Ga wasu daga cikin falalar azumin watan Ramadan:
1. Ana buɗe kofofin Aljanna, ana rufe ƙofofin wuta, kuma ana ɗaure shaiɗanu. Wannan yana taimaka wa zuciyar Musulmi wajen yin alheri da kauce wa munanan ayyuka.
2. Yin azumi da tsayuwar sallar Tarawihi saboda Allah da neman lada, ana gafarta zunuban bawa da suka gabata.
3. Akwai daren Lailatul-Kadari, wanda ya fi wata dubu daraja. Duk wanda ya yi ibada a wannan dare yana mai imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa na baya.
4. Yin Umara a watan Ramadan yana daidai da yin aikin Hajji tare da Manzon Allah (SAW).
5. Watan Ramadan wata ne na Alƙur’ani, saboda a cikinsa aka saukar da shi. Don haka, ya dace a yawaita karanta shi.
6. Watan Ramadan wata ne na kyauta, ciyarwa da sadaka. Manzon Allah (SAW) ya fi yawan kyauta a wannan wata.
7. Baccin mai azumi ibada ne, domin yana rage sha’awa da kula da zuciya.
8. Mai azumi yana da farin ciki biyu:
Yayin da zai buɗe baki bayan azumi. Lokacin da zai haɗu da Allah (S.W.A.) ranar alƙiyama.9. Azumi garkuwa ne daga wutar Jahannama. Yana kare mutum daga sharrin sha’awa da zunubi.
10. A Ramadan, Allah Yana ’yantar da bayinsa daga wuta. Duk wani dare, Allah Yana yafe wa bayinsa kuma yana kuɓutar da su daga azabar lahira.
Wannan wata mai albarka yana ƙarfafa imani, ibada, da kyautatawa.
Don haka, ya kamata Musulmi su yi amfani da watan Ramadan don samun kusanci ga Allah da aikata kyawawan ayyuka.