Aminiya:
2025-04-02@15:28:55 GMT

Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi

Published: 2nd, March 2025 GMT

’Yan sanda sun cafke wani magidanci mai shekaru 50, Alhaji Nuru Isah kan zargin lakaɗa wa matarsa dukan da ya yi ajalinta a dalilin abincin buɗa-baki.

Bayanai sun ce taƙaddamar wadda aka soma gudanar da bincike a kanta ta auku ne a ranar Asabar a yankin Fadaman Mada da ke Jihar Bauchi.

Burina in yi fice kamar mahaifiyata — Maryam ‘Yar Auta Abubuwan da ya kamata a sani game da azumin watan Ramadana

Kakakin rundunar, CSP Ahmed Mohammed Wakil ya ce, “saɓani ne ya kaure tsakanin wani mai suna Nuru Isah mai shekara 50 da matarsa ta biyu, Wasila Abdullahi kan tsarin abinci da kayan buɗa-baki na gidan.

’Yan sanda sun ce bincike farko na nuna cewa mijin ya yi amfani da bulala wajen bugun matar mai shekaru 24, “inda ta yanke jiki ta faɗi, da aka kai ta asibitin koyarwa na jami’ar Tafawa Ɓalewa ne likitoci suka tabbatar da rasuwarta.”

Sanarwar ta ƙara da cewa ’yan sanda sun kama mijin, sun ɗauko bulalar da aka yi amfani da ita, sannan kuma za a yi binciken ƙwaƙwaf a kan gawar.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Auwal Musa Muhammad, ya bayyana cewa za a gudanar da bincike domin tabbatar da adalci a lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Azumin Ramadan Jihar Bauchi

এছাড়াও পড়ুন:

Pezeshkian: Iran Ba Za Ta Yi Tattaunawa Kai Tsaye Da Amurka Ba

Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa, Iran ba ta shiga tattaunawa da Amurka kai tsaye ba, yana mai mayar da martini kan wasikar da shugaban Amurka ya aike mata, amma kuma ya bayyana cewa hakan zai bude kofa ga tattaunawar kai tsaye.

Da yake magana a wani taron majalisar ministocin a ranar Lahadi, Pezeshkian ya tabbatar da cewa an isar da martanin Iran ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump ta hanyar Oman.

Ya jaddada cewa, yayin da Iran ta yi watsi da tattaunawar kai tsaye, ba ta taba rufe kofar yin shawarwarin kai tsaye ba matukar dai aka cimma wani abu da bai yi karo da manufofin Iran ba.

Ya kara da cewa, “Kamar yadda Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta taba toshe hanyoyin yin shawarwari kai tsaye a baya ba, amsar wasikar ta kara tababtar da hakan, tare da tabbatar da cewa sakamakon tattaunawar da za a yi wadda ba ta kai tsaye ba, it ace za ta fayace yiwuwar yin tattanawar ta kai tsaye ko akasin hakan.

Shugaban na Iran ya alakanta kalubalen da ake fuskanta a tsarin tattaunawar da rashin matsaya guda daga bangaren Amurka, yana mai jaddada cewa dole ne Amurka ta gyara kura-kuran da aka yi a baya tare da maido da aminci da gaskiya da kuma cika alkawali.

Pezeshkian ya yi nuni da cewa, “Wannan zai zama gwaji a kan n yadda Amurkawa za su iya tabbatar da ci gaban tattaunawar.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Ramuwar Gayya Kan Takunkumin Biza Da Amurka Ta Kakaba Wa Jami’anta
  • Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha
  • Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha
  • Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji
  • HOTUNA: Abba da Gwamnan Edo sun ziyarci iyalan mafarautan da aka kashe a Edo
  • Gwamna Abba Ya Nemi A Bayyana Fuskokin Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Hadin Gwiwar Inganta Amfani Da AI Don Amfanar Da Kowa
  • Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano
  • Pezeshkian: Iran Ba Za Ta Yi Tattaunawa Kai Tsaye Da Amurka Ba
  • Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba