Aminiya:
2025-03-03@09:20:14 GMT

Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Edo

Published: 2nd, March 2025 GMT

Aƙalla fasinjoji 12 ne suka ƙone ƙurmus har lahira a wani mummunan hatsari da ya auku a kan titin Benin zuwa Auchi a Jihar Edo.

Kakakin Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC) a Edo, Cyril Mathew, ya tabbatar da aukuwar hatsarin.

Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi Abubuwan da ya kamata a sani game da azumin watan Ramadana

Ya ce wata mota ƙirar Toyota Hiace ce ta yi karo da babbar tifa.

A cewarsa, hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5 na asuba a ranar Asabar, a kusa da wani shingen sojoji da ke yankin Igueoviobo.

“Motar ta taso ne daga Zuba a Babban Birnin Tarayya tana kan hanyarta n zuwa Benin, amma ta yi karo da wata babbar tifa da ke kan hanyar zuwa Auchi.

“Duk fasinjojin da ke cikin motar sun rasa rayukansu,” in ji shi.

Mathew, ya ce ana zargin direban motar da gajiya yayin tuƙi, lamarin da ya sa ya fara barci a kan hanya, wanda hakan ya haddasa hatsarin.

Karon da motocin suka yi ya haddasa tashin wuta, lamarin da ya sanya fasinjojin zuka ƙone ƙurmus.

Sai dai direban babbar tifar da yaronsa sun tsira ba tare da sun ji rauni ba.

Kakakin ya shawarci direbobi da suke hutawa a duk lokacin da suka gaji domin gujewa aukuwar hatsari.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Mu ne muka kai samame otal ba ’yan bindiga ba — EFCC

Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta ce ita ce ta kai samame otal ɗin White Hill da ke kan titin Shiroro a Minna, Babban Birnin Jihar Neja.

A yayin farmakin, an kama aƙalla baƙi 10 da ake zargi da aikata damfara a Intanet, wanda aka tafi da su Kaduna.

Girke-girken Azumi: Yadda ake yin Tsiren Dankali Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Edo

Wani ma’aikacin otal ɗin da ya nemi a sakaya sunansa, ya musanta jita-jitar da ake yaɗawa cewar ’yan bindiga ne suka yi basaja a kayan EFCC, sula sace baƙi 10 a ranar 27 ga watan Fabrairu.

“Ba ’yan bindiga ba ne. Jami’an EFCC ne suka zo suka kama wasu ‘yan damfara suka tafi da su Kaduna,” in ji shi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya kuma yi watsi da wannan jita-jitar.

Ya shawarci ’yan jarida su tuntuɓi EFCC domin tabbatar da sahihancin lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mu ne muka kai samame otal ba ’yan bindiga ba — EFCC
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Xi Ya Jaddada Ciyar Da Shirin Kasar Sin Mai Kwanciyar Hankali Zuwa Babban Mataki
  • Yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasuwannin Arewa
  • Gobara ta ƙone sashen wani asibiti a Legas
  • Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno
  • ‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina
  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu