Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano
Published: 2nd, March 2025 GMT
Hukumar Hisba ta Jihar Kano, ta kama wasu matasa da ba su yi azumi a ranar farko ta watan Ramadan ba.
Mataimakin Kwamanda Janar na Hukumar, Dokta Mujahideen Abubakar ne, ya tabbatar da kama matasan.
Sojoji sun ƙwato makamai a dajin Sambisa Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a BauchiHakazalika, ya tabbatar da cewa jami’an Hisba sun cafke su yayin sintiri da suka yi a sassa daban-daban na Kano.
Har ila yau, hukumar ta kama wasu matasa ku san 60 bisa laifin askin banza, wanda ta ce ya saɓa wa dokokin addini da al’ada.
Bugu da ƙari, an kama wasu direbobin Adaidaita Sahu da ake zargi da cakuɗa maza da mata a cikin abin hawa, abin da hukumar ta ce ba za ta yarda da shi ba.
Hisba ta ce za ta ci gaba da sintiri domin tabbatar da an kiyaye dokokin Shari’a a lokacin watan Ramadan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga, Sun Ceto Ɗalibai 2 A Nasarawa
Da suka ga cewa ba za su yi nasara ba, sai suka tsere suka bar waɗanda suka sace.
An kama mutum ɗaya, Ibrahim Musa, mazaunin ƙauyen Abuni a Ƙaramar Hukumar Awe.
Ya ya bayar da muhimman bayanai da ke taimakawa wajen bincike.
Kwamishinan ya jinjina wa jami’an rundunar yaƙi da garkuwa da mutane bisa ƙoƙarinsu kuma ya jaddada aniyar ‘yansanda na yaƙi da aikata laifuka.
Ya buƙaci jami’ansa da su ci gaba da jajircewa don tabbatar da tsaro a jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp