Aminiya:
2025-04-23@06:36:11 GMT

Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano

Published: 2nd, March 2025 GMT

Hukumar Hisba ta Jihar Kano, ta kama wasu matasa da ba su yi azumi a ranar farko ta watan Ramadan ba.

Mataimakin Kwamanda Janar na Hukumar, Dokta Mujahideen Abubakar ne, ya tabbatar da kama matasan.

Sojoji sun ƙwato makamai a dajin Sambisa Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi

Hakazalika, ya tabbatar da cewa jami’an Hisba sun cafke su yayin sintiri da suka yi a sassa daban-daban na Kano.

Har ila yau, hukumar ta kama wasu matasa ku san 60 bisa laifin askin banza, wanda ta ce ya saɓa wa dokokin addini da al’ada.

Bugu da ƙari, an kama wasu direbobin Adaidaita Sahu da ake zargi da cakuɗa maza da mata a cikin abin hawa, abin da hukumar ta ce ba za ta yarda da shi ba.

Hisba ta ce za ta ci gaba da sintiri domin tabbatar da an kiyaye dokokin Shari’a a lokacin watan Ramadan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar

Iran ta sanar da dage tattaunawar da aka shirya gudanarwa yau Laraba tsakanin tawagar kwararu ta kasar da kuma na Amurka a kasar Oman a wani bangare na ci gaba da tattaunawar da ake tsakanin kasashen biyu kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ya bayyana cewa, an dage tattaunawar ta matakin kwararru tsakanin Iran da Amurka kan cikakkun bayanai na fasaha na yiwuwar maye gurbin yarjejeniyar nukiliyar shekarar 2015, wadda aka shirya yi a yau ranar Laraba, zuwa ranar mai zuwa 26 ga watan Afrilu.

Esmaeil Baghaei ya bayyana cewa, za a gudanar da taron a daidai lokacin zagaye na gaba na tattaunawar tsakanin jagororin tawagogin guda biyu.

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi da Steve Witkoff, manzon musamman na shugaban Amurka kan harkokin yankin gabas ta tsakiya, sun jagoranci tattaunawar wacce ba ta kai tsaye ba har sau  biyu kan shirin nukiliyar Iran da kuma dage takunkumin da Amurka ta kakaba wa Iran a babban birnin Oman na Muscat da babban birnin Italiya, Roma, a ranakun 12 da 19 ga watan Afrilun nan, a shiga tsakanin Ministan harkokin wajen Omani Badr bin Hamad Al Busaidi ne ya shiga tsakani tattaunawar.

A ranar 26 ga watan Afrilu ne ake sa ran gudanar da zagaye na uku na shawarwarin kai tsaye tsakanin Araghchi da Witkoff a kasar Oman domin tantance sakamakon tarukan da masana suka yi da kuma auna yadda suke kusa da cimma matsaya.

A wani labara kuma, ministan harkokin wajen Iran, Araghchi ya tattauna da shugaban hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya, ta IAEA, jiya Talata

Inda ya yi masa bayani kan sabbin abubuwan da suka faru game da tattaunawar da Amurka, yana mai jaddada kudurin Iran na yin shawarwarin bil hakki.

Shi ma Grossi, ya yaba da matakin da Iran ta dauka, ya kuma bayyana shirin hukumar na bayar da duk wani taimako a cikin wannan tsari, daidai da ayyukanta da ikonta kamar yadda dokar hukumar ta IAEA ta ayyana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar
  • Hajjin 2025: Sahun Farko Zai Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki 9 Ga Watan Mayu
  • Za’a Yi Zana’izar Paparoma Francis A Ranar Asabar 26 Ga Watan Afrilu
  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano
  • Shettima Ya Gayyaci Shugaban NAHCON Da Mambobin Hukumar Kan Shirye-shiryen Hajjin 2025
  • An tsinci gawar saurayi da buduwarsa a tube a cikin daki
  • Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI
  • NDLEA Ta Kama Masu Sayar Da Kwaya Ga Ƴan Bindiga A Kano
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Bada Tallafin Kudi Ga Manoman Alkama
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya