Aminiya:
2025-04-02@12:16:53 GMT

Mahara sun yi basaja da kayan EFCC wajen sace mutum 10 a otal

Published: 2nd, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi basaja a matsayin jami’an Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), tare da sace mutum 10 a Otal ɗin White Hill da ke kan titin Shiroro a Ƙaramar Hukumar Chanchaga a Jihar Neja.

Wani masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 4:58 na asubar ranar Talata, 27 ga watan Fabrairu, 2025.

Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun isa otal ɗin ne, inda suka yi basaja a matsayin jami’an EFCC da ke bakin aiki.

Sun fara da kashe na’urorin CCTV na otal ɗin kafin su kutsa cikin ɗakunan baƙi, inda suka kwashe mutum 10 suka tafi da su ba tare da sanin inda suka nufa ba.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ya ce suna gudanar da bincike don gano waɗanda suka aikata laifin da kuma ceto waɗanda aka sace.

Hukumomi sun buƙaci jama’a da su kasance masu sanya ido tare da sanar da hukumomin tsaro idan sun ga wani abin da ke da ɗaukar hankali.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa hari Jami an Tsaro kaya mahara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Abba Ya Nemi A Bayyana Fuskokin Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo

Haka kuma, ya yaba wa Gwamna Okpebholo bisa tattaunawarsa da shugabannin al’ummar Hausa a Edo domin hana rikici da kuma alƙawarin biyan diyya ga iyalan mamatan.

“Biyan diyya da aka alƙawarta abu ne mai kyau, amma dole ne a tabbatar da hakan cikin gaggawa domin taimaka wa iyalan da suka rasa masu ɗaukar nauyinsu,” ya ƙara da cewa.

A nasa ɓangaren, Gwamna Okpebholo ya nuna matuƙar damuwarsa kan wannan kisa, inda ya tabbatar da cewa za a hukunta waɗanda suka aikata laifin.

“Ina samu labarin abin da ya faru, na garzaya zuwa Uromi. Na gana da al’ummar Hausa a wajen, kuma mun yi ƙoƙarin kwantar da tarzoma.

“Ina tabbatar muku da cewa za a hukunta waɗanda suka aikata wannan ta’asa,” in ji shi.

Gwamnatin Jihar Kano, ta jaddada buƙatar a tabbatar da adalci domin dawo da kwanciyar hankali da hana aukuwar irin wannan rikici a gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatan Kasar Sin Sun Ceto Mutum 8 Zuwa Yanzu A Myanmar
  • Wang Yi Ya Jinjina Wa Gudummawar Da Sinawa Da ’Yan Rasha Suka Bayar A Yakin Duniya Na Biyu
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • Gwamna Edo Okpebholor Ya Jajantawa Iyalan Wadanda Aka Kashe
  • Gwamna Abba Ya Nemi A Bayyana Fuskokin Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Yadda ‘Yan Banga A Edo Suka Yi Sanadin Kashe Matafiya Mafarauta 16 – Direban Motar
  • Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi
  • Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo