Aminiya:
2025-04-22@17:51:50 GMT

Mahara sun yi basaja da kayan EFCC wajen sace mutum 10 a otal

Published: 2nd, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi basaja a matsayin jami’an Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), tare da sace mutum 10 a Otal ɗin White Hill da ke kan titin Shiroro a Ƙaramar Hukumar Chanchaga a Jihar Neja.

Wani masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 4:58 na asubar ranar Talata, 27 ga watan Fabrairu, 2025.

Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun isa otal ɗin ne, inda suka yi basaja a matsayin jami’an EFCC da ke bakin aiki.

Sun fara da kashe na’urorin CCTV na otal ɗin kafin su kutsa cikin ɗakunan baƙi, inda suka kwashe mutum 10 suka tafi da su ba tare da sanin inda suka nufa ba.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ya ce suna gudanar da bincike don gano waɗanda suka aikata laifin da kuma ceto waɗanda aka sace.

Hukumomi sun buƙaci jama’a da su kasance masu sanya ido tare da sanar da hukumomin tsaro idan sun ga wani abin da ke da ɗaukar hankali.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa hari Jami an Tsaro kaya mahara

এছাড়াও পড়ুন:

Darajar Cinikin Sarin Kaya Da Sayen Kayan Masarufin Sin Ta Karu Da Dala Biliyan 452.5 a Rubu’In Farkon Bana

Ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta tabbatar da tsare-tsaren da kwamitin tsakiyar jam’iyyar kwaminis ta Sin da majalisar gudanarwar kasar suka tsayar don gaggauta kyautata tsarin tafiyar da ciniki daidai da zamani, da ingiza ingantaciyar bunkasuwar cinikin sarin kaya da sayen kayan masarufi bisa matakai daban-daban. Bisa alkaluman da hukumar kididdigar Sin ta fitar a rubu’in farko wato daga watan Janairu zuwa Maris na bana, darajar wadannan bangarori ta karu da dalar biliyan 452.5 a wadannan watanni uku, wanda ya karu da kashi 5.8% bisa na makamancin lokacin bara, kana adadin ya kai kashi 10.4% bisa na dukkan GDPn kasar.

 

Nagartacciyar bunkasar wadannan sana’o’i na nuna goyon baya na tsarin habaka bukatu cikin gidan kasar da tafiyar da tattalin arzikin al’umma ba tare da tangarda ba. (Amina Xu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • Motar hatsi ta kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Motar hatsi kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Darajar Cinikin Sarin Kaya Da Sayen Kayan Masarufin Sin Ta Karu Da Dala Biliyan 452.5 a Rubu’In Farkon Bana
  • Abubuwan da suka sa Fafaroma Francis ya yi fice a duniya
  • Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja
  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • Ruftawar gini ta kashe mutum 5 a Legas
  • Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar