Iran: Majalisar dokoki ta tsige ministan tattalin arziki saboda hauhawar farashi
Published: 2nd, March 2025 GMT
‘Yan majalisar dokokin kasar Iran sun kada kuri’ar tsige ministan harkokin tattalin arziki da kudi Abdonnasser Hemmati daga mukaminsa saboda matsalolin tattalin arziki da kuma faduwar darajar kudin kasar.
Hemmati ya rasa kuri’ar amincewa a zaman majalisar na wannan Lahadi inda ‘yan majalisa 182 daga cikin 273 suka kada kuri’ar tsige shi.
A yayin Zaman ministan da kansa da shugaban kasar Masoud Pezeshkian sun halarci wurin, yayin da kuma ‘yan majalisar kan batun kudurin, amma dai kudirin ya wuce bayan samun rinjayen amincewa da shi.
Shugaba Pezeshkian ya kare Hemmati, tsohon gwamnan babban bankin kasar Iran, ya kuma ce kasar na cikin yakin tattalin arziki da makiya, kuma zargin juna ba zai magance wata matsala ba.
Ya jaddada cewa hadin kai da hadin gwiwa ne kadai mafita ga matsalolin da kasar ke fuskanta.
Hemmati ya kuma yi jawabi a zaman inda ya ce Iran na da karfin iko kuma za ta yi nasara a yakin tattalin arzikin makiya.
Wasu gungun ‘yan majalisa 91 ne suka fara shirin tsige Hemmati, saboda gazawarsa wajen daidaita kasuwanni da kuma dakile hauhawar farashin kayayyaki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tattalin arziki
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Jana’izar Shahidan Hizbullah Fiye Da 100 A Kudancin Lebanon
A jiya Juma’a ne dai aka yi jana’izar shahidan Hizbullah 130 a garuruwan Aytas-sha’ab da Aytarun da suke da kudancin Lebanon.
Tashar talabijin din al-manar ta watsa taron jana’izar shahidai 95 da su ka yi shahada watanni uku da su ka gabata a yayin yaki da HKI.
A garin Aytrun da shi ma yake a kudancin Lebanon an yi jana’izar shahidai 35.
Dukkkanin jana’izar biyu ta sami halartar dububan mutane daga cikin garuruwan da kuma wajensu.
A gefe daya, a daidai lokacin da ake gudanar da jana’izar mutanen a garin Aytatun, sojojin HKI sun kai hari a gefen garin, sai dai babu rahoto akan shahada ko jikkatar mutane.
Dan majalisa mai wakilntar Hizbullah a majalisar dokoki Hassan Fadlallah wanda kuma shi ne shugaban bangaren masu goyon bayan gwgawarmaya a majalisar, ya gabatar da jawabi a wurin jana’izar, inda ya bayyana cewa; Shahidan sun kwanta dama ne a fagen dagar kare daukakar al’ummar Lebanon.
A garin Aytas-sha’ab, an yi taho mu gama mai tsanani a tsakanin dakarun Hizbullah da sojojin mamayar HKI a lokacin yakin 2006, kuma a wannan yakin ma abinda ya faru kenan,’kamar yadda Fadlallah ya bayyana.
Dan majalisar ya kuma jaddada cewa; Za a sake gina wannan garin, kuma yin hakan nauyi ne da ya rataya a wuyan gwamnatin Lebanon.