Aminiya:
2025-03-03@09:29:35 GMT

Girke-girken Azumi: Yadda ake yin Tsiren Dankali

Published: 2nd, March 2025 GMT

Yau a filin namu na Girke-girken Azumi za mu kawo muku yadda ake yin Tsiren Dankali.

Za a iya amfani da girkin namu na yau a matsayin abin buɗa-baki, da zarar an sha ruwa.

Mahara sun yi basaja da kayan EFCC wajen sace mutum 10 a otal Sojoji sun ƙwato makamai a dajin Sambisa

Ga kayan hadin da ake bukata don yin girkin:

Dankali Turawa Nikakken nama Man gyada Sinadarin ɗanɗano Kori Tyme Tafarnuwa Tsiken tsire Yadda ake hada shi

A samu nikakakken nama sai a hada da kayan kamshi(kori, tyme da tafarnuwa) da sinadarin ɗanɗano.

Idan ya hadu sai a gutsira a fadada shi yadda zai yi falan-falan sai a ajiye shi a gefe.

Sannan a dauko dankali sai a fere shi, a yayyanka shi kamar kwabo.

Sai a dauko tsinken tsire a jera dankalin a jiki tare da hadadden nikakken naman.

Idan an sa dankali a jikin tsinken sai a dauko wannan nikakken naman a sa shi a jiki daidai fadin dankalin sannan sai a sake sa dankalin sai a sa naman.

Haka za a yi, har sai tsinken ya cika.

Amma a tabbatar dankalin da aka yanka ya kasance guda daya, ma’ana sai kin gama da guda daya, sannan za a sake yanka wani don kada ya hargitse wajen dankalin a jikin tsinken.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a Borno

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno, ta sanar da ƙarin matakan tsaro yayin da al’ummar Musulmi suka shiga watan azumin Ramadan.

Haka kuma, rundunar ta taya Musulmi murnar shigowar wannan wata mai alfarma.

Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya

Kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana cewa an kammala shirin tsaurara tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a cikin watan Ramadan.

“Mun san muhimmancin wannan wata ga ’yan uwanmu Musulmi,” in ji sanarwar.

“Saboda haka, mun ƙara sintiri da samar da jami’an tsaro a wurare masu muhimmanci a faɗin jihar.”

Kwamishinan ’yan sandan Borno, CP Yusufu Mohammed Lawal, ya tabbatar da cewa rundunar tana sadaukar da kai domin kare lafiyar jama’a a cikin wannan wata.

“Burinmu shi ne kowa ya samu damar gudanar da ibadarsa cikin kwanciyar hankali da tsaro,” in ji Kwamishinan.

Haka kuma, rundunar ta buƙaci jama’a da su kasance masu lura tare da kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba ga ofishin ’yan sanda mafi kusa.

“Idan kun ga wani abu, ku sanar da hukuma,” in ji ASP Daso.

Rundunar ta kuma fitar da lambobin kiran kar ta kwana domin bayar da rahoto: 08068075581 da 08023473293.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Yadda za ku yi girke-girken azumi da kuɗi kaɗan
  • Mahara sun yi basaja da kayan EFCC wajen sace mutum 10 a otal
  • Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano
  •  Hamas: Matakin Netenyahu Na Dakatar Da Shigar Kayan Agaji Cikin Gaza Keta Yarjejeniya Ne
  • Abubuwan da ya kamata a sani game da azumin watan Ramadana
  • Yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasuwannin Arewa
  • Girke-girkenmu Na Azumi
  • Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a Borno
  • Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya